ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Wanda Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani, Shi Ma Sai An Hukunta Shi – Gwamna Sule 

by Sulaiman
1 year ago
Sule

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya sha alwashin zakulo duk wadanda suke da hannu a rikincin da ya barke a garin Mararraba Udege da kauyen Oduh a makon da ya gabata.

 

Ya ce, “hakkin Gwamnati ne ta samar da zaman lafiya da kare dukiyoyin al’umma, don haka, duk wanda aka samu da hannu a wannan rikicin za a mika shi gaban kotu ta yi masa hukunci daidai da abinda ya aikata.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yansanda Sun Cafke Baƙin Haure 165, An Miƙa Wa Hukumar NIS A Kebbi
  • Kuɗin Fansa ₦13m, Kasonsa ₦200,000: Ɗan Shekara 50 Ya Jagoranci Garkuwa Da Ɗansa Da Iyalansa 

“Abin bakin ciki ne mutanen da suke ‘yan kabila daya, Asali daya, Uwa daya, Uba daya amma suna kashe junansu saboda son zuciya da kwadayin abin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Wannan jahilci ne, babu yadda mai hankali zai yarda ya kashe dan uwanshi saboda abin duniya.

 

“Babu wata kabila da ake kira Afon dutsi ko Afon kasa. Duk sunansu AFO.  Ya kuma janyo hankalin matasa da su daina yarda ‘yan siyasa batagari na amfani da su wajen neman biyan bukatar kansu, suna sanya su kashe junansu ko kona gidajen al’umma.”

 

Gwamna Abdullahi Sule ya kara da cewa, ya je kasar Sin don tattaunawa da kamfanin hakar Ma’adanai na ‘Juling Lithium Nasarawa Lithium Project’ a birnin Beijing, don ganin yadda kamfanin zai sake habaka basirar ma’aikata Leburori da ke aiki a kamfanin da ke Udege. Ganin cewa, ma’aikatan fiye da shekaru 20,  aikin leburanci kawai suke yi babu ci gaba, don haka, dole a samu sauyi.

 

“Na tattauna da manyan Shugabannin kamfanin Shneyen. Nace sama da shekara 20 kuna hakar ma’adinan Tantalaye a Udege kuna tafiya da shi. Amma mutanen Udege baya ga aikin leburanci babu wani aikin da kuka basu. saboda haka, yanzu me zaku yi Wanda matasan gurin zasu samu aikin yi? Wannan maganar ta tabasu sosai. Nan take suka ce, za su gina katafaren kamfani da za a dauki matasa aiki a koyar dasu ilimin yadda ake sarrafa Ma’adinai da sauransu.

 

“Don haka, bai dace a kawo hargitsin da zai yi sanadin kulle wannan kamfani da wannan alherin da ke shirin zuwa wannan yankin ba, saboda banbancin siyasa.”

 

Shima a nasa jawabin OSu- Ajiris na Udege Mbeki Dr. Alhaji Halilu Bala ya yi godiya ga Gwamna Abdullahi Sule da ya yi tattaki da tawagarsa yazo ya gane wa idanunsa kuma ya dauki matakin da ya dace.

 

Sarkin yayi kira ga wadanda aka yi wa barna da su kara hakuri, doka za ta yi aiki kan duk wanda aka kama da hannu kan tayar da rikicin.

Sule
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

Gobara Ta Tashi A Wata Makarantar Allo Ta Hallaka Mutum 17, Ta Jikkata 16 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.