• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan Ganin An Tabbatar Da “Faster, Higher, Stronger –Together” A Wasannin Olympics Na Los Angeles

by Lubabatu Lei
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Duniya Na Fatan Ganin An Tabbatar Da “Faster, Higher, Stronger –Together” A Wasannin Olympics Na Los Angeles
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gun taron manema labarai da kwamitin kula da wasannin Olympics na lokacin zafi na birnin Los Angeles ya kira a kwanan baya, ‘yan jaridar kasashe da dama sun yi tambayoyin da suka shafi batun siyasantar da wasanni, da batun bindiga da ma tsaro da sauransu, kuma damuwar da ‘yan jaridar suka nuna a tambayoyinsu ta shaida yadda kasar Amurka ta dade tana dakile abokan takararta ta hanyoyin da ba su dace ba, da ma yadda take kokarin fadada nuna fin karfi har zuwa fagen wasanni.

Gasar wasannin Olympics karo na 33 da aka kammala ba da jimawa ba a birnin Paris, ta sake shaida yadda Amurka ta yi ta siyasantar da harkar wasanni. Tun wasu watanni kafin a fara gasar, wasu hukumomi da ma kafofin yada labarai na kasar suka yi ta samar da rahotannin wai ‘yan wasan ninkaya na kasar Sin sun sha maganin kara kuzari, ba tare da yin la’akari da sakamakon bincike mai adalci da kungiyar kula da wasannin ninkaya ta duniya da hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta duniya(WADA) suka samar ba, sai kuma bayan da aka fara gasar, suka yi ta shafa bakin fenti ga ‘yan wasan kasar Sin da suka ci nasara. Baya ga haka, wasu ‘yan majalisun dokoki na kasar Amurka sun kuma gabatar da shirin doka ta wai “farfado da imani ga hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta duniya”, inda suka yi barazanar daina samar da kudin tallafi na sama da dala miliyan uku da ya kamata gwamnatin kasar Amurka ta biya hukumar a kowace shekara.

A sa’in da Amurka ke yada karairayi na zargin ‘yan wasa na wasu kasashe da shan maganin kara kuzari, a sa’i daya kuma, sun ba da kariya ga ‘yan wasansu da gwajin da aka yi musu ya shaida cewa sun sha sinadaran kara kuzari. Sanarwar da hukumar WADA ta bayar a kwanan baya ta nuna cewa, hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta kasar Amurka ta shafe shekaru da dama tana amincewa da ‘yan wasa da suka sha maganin su halarci wasannin.

Har kullum Amurka tana kallon kanta a matsayin kasar da ta fi karfi a fannin wasanni, wadda kuma take daukar wasanni a matsayin wani muhimmin bangare na karfinta. Sai dai yayin da kasar Sin da sauran kasashe suka yi ta samun ci gaba a fannin wasanni a cikin ‘yan shekarun baya, har suka zarce Amurka a wasu wasannin da a baya Amurka ta yi fice, misali wasannin guje-guje da tsalle-tsalle da ninkaya da sauransu, lamarin ya kara sa Amurka damuwa. Don haka, ta kwaikwayi matakan da ta saba na dakile kasar Sin a fannonin siyasa da tattalin arziki, ta yi ta yada karairayi don shafa wa kasar Sin da ‘yan wasanta kashin kaza, don karfafa matsayinta a fannin.

“Karin sauri da karin girma da karin karfi, da kuma karin hadin kai” shi ne taken wasannin Olympics. Takara da juna ba shi ne jigo daya kacal na wasannin Olympics ba, a maimakon haka, wasannin Olympics sun fi shafar “hadin kai da zumunta”, da ma burin da ‘yan Adam ke neman cimmawa na zaman lafiya da hadin kai da ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

A gasar wasannin Olympics na Paris, yadda ‘yar wasan Badminton ta kasar Sin malama He Bingjiao ta dauki bajin kwamitin wasannin Olympics na kasar Spaniya a lokacin da aka mika mata lambar yabo, don isar da gaisuwa da fatan alheri ga abokiyar takararta Carolina Marín Martin ‘yar kasar Spaniya, wadda ta janye jiki daga gasar sabo da raunukan da ta ji, da ma yadda ‘yan wasannin kwallon tebur na kasashen Sin da Koriya ta arewa da Koriya ta kudu suka dauki hoto tare a lokacin da aka mika musu lambobin yabo, da dai sauransu, duk sun bayyana wa duniya abun da ake nufi da wasannin Olympics.

  • Na’urar Bincike Ta Karkashin Teku Ta Kasar Sin Ta Kammala Nutsu A Karo Na 300

Nan da shekaru hudu masu zuwa, za a gudanar da gasar wasannin Olympics na lokacin zafi karo na 34 a birnin Los Angeles na kasar Amurka, kuma daina siyasantar da wasanni ita ce bukata da buri na bai daya na kasashen duniya game da gasar. Muna fatan kwamitin kula da wasannin Olympics na Los Angeles za su samar wa ‘yan wasa wani dandali mai adalci da hadin kai da zumunci, don ‘yan wasa na kasa da kasa su nuna kwarewarsu, kuma kasashen da ke fama da baraka da rikice-rikice su sake hada kansu karkashin ruhin wasannin Olympics. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaDuniyaGasaOlympicsWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Vietnam

Next Post

Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Sojoji

Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.