ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duniya Na Fatan Ganin An Tabbatar Da “Faster, Higher, Stronger –Together” A Wasannin Olympics Na Los Angeles

by Lubabatu Lei
2 years ago
olympics

A gun taron manema labarai da kwamitin kula da wasannin Olympics na lokacin zafi na birnin Los Angeles ya kira a kwanan baya, ‘yan jaridar kasashe da dama sun yi tambayoyin da suka shafi batun siyasantar da wasanni, da batun bindiga da ma tsaro da sauransu, kuma damuwar da ‘yan jaridar suka nuna a tambayoyinsu ta shaida yadda kasar Amurka ta dade tana dakile abokan takararta ta hanyoyin da ba su dace ba, da ma yadda take kokarin fadada nuna fin karfi har zuwa fagen wasanni.

Gasar wasannin Olympics karo na 33 da aka kammala ba da jimawa ba a birnin Paris, ta sake shaida yadda Amurka ta yi ta siyasantar da harkar wasanni. Tun wasu watanni kafin a fara gasar, wasu hukumomi da ma kafofin yada labarai na kasar suka yi ta samar da rahotannin wai ‘yan wasan ninkaya na kasar Sin sun sha maganin kara kuzari, ba tare da yin la’akari da sakamakon bincike mai adalci da kungiyar kula da wasannin ninkaya ta duniya da hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta duniya(WADA) suka samar ba, sai kuma bayan da aka fara gasar, suka yi ta shafa bakin fenti ga ‘yan wasan kasar Sin da suka ci nasara. Baya ga haka, wasu ‘yan majalisun dokoki na kasar Amurka sun kuma gabatar da shirin doka ta wai “farfado da imani ga hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta duniya”, inda suka yi barazanar daina samar da kudin tallafi na sama da dala miliyan uku da ya kamata gwamnatin kasar Amurka ta biya hukumar a kowace shekara.

A sa’in da Amurka ke yada karairayi na zargin ‘yan wasa na wasu kasashe da shan maganin kara kuzari, a sa’i daya kuma, sun ba da kariya ga ‘yan wasansu da gwajin da aka yi musu ya shaida cewa sun sha sinadaran kara kuzari. Sanarwar da hukumar WADA ta bayar a kwanan baya ta nuna cewa, hukumar yaki da shan maganin kara kuzari ta kasar Amurka ta shafe shekaru da dama tana amincewa da ‘yan wasa da suka sha maganin su halarci wasannin.

ADVERTISEMENT

Har kullum Amurka tana kallon kanta a matsayin kasar da ta fi karfi a fannin wasanni, wadda kuma take daukar wasanni a matsayin wani muhimmin bangare na karfinta. Sai dai yayin da kasar Sin da sauran kasashe suka yi ta samun ci gaba a fannin wasanni a cikin ‘yan shekarun baya, har suka zarce Amurka a wasu wasannin da a baya Amurka ta yi fice, misali wasannin guje-guje da tsalle-tsalle da ninkaya da sauransu, lamarin ya kara sa Amurka damuwa. Don haka, ta kwaikwayi matakan da ta saba na dakile kasar Sin a fannonin siyasa da tattalin arziki, ta yi ta yada karairayi don shafa wa kasar Sin da ‘yan wasanta kashin kaza, don karfafa matsayinta a fannin.

“Karin sauri da karin girma da karin karfi, da kuma karin hadin kai” shi ne taken wasannin Olympics. Takara da juna ba shi ne jigo daya kacal na wasannin Olympics ba, a maimakon haka, wasannin Olympics sun fi shafar “hadin kai da zumunta”, da ma burin da ‘yan Adam ke neman cimmawa na zaman lafiya da hadin kai da ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A gasar wasannin Olympics na Paris, yadda ‘yar wasan Badminton ta kasar Sin malama He Bingjiao ta dauki bajin kwamitin wasannin Olympics na kasar Spaniya a lokacin da aka mika mata lambar yabo, don isar da gaisuwa da fatan alheri ga abokiyar takararta Carolina Marín Martin ‘yar kasar Spaniya, wadda ta janye jiki daga gasar sabo da raunukan da ta ji, da ma yadda ‘yan wasannin kwallon tebur na kasashen Sin da Koriya ta arewa da Koriya ta kudu suka dauki hoto tare a lokacin da aka mika musu lambobin yabo, da dai sauransu, duk sun bayyana wa duniya abun da ake nufi da wasannin Olympics.

  • Na’urar Bincike Ta Karkashin Teku Ta Kasar Sin Ta Kammala Nutsu A Karo Na 300

Nan da shekaru hudu masu zuwa, za a gudanar da gasar wasannin Olympics na lokacin zafi karo na 34 a birnin Los Angeles na kasar Amurka, kuma daina siyasantar da wasanni ita ce bukata da buri na bai daya na kasashen duniya game da gasar. Muna fatan kwamitin kula da wasannin Olympics na Los Angeles za su samar wa ‘yan wasa wani dandali mai adalci da hadin kai da zumunci, don ‘yan wasa na kasa da kasa su nuna kwarewarsu, kuma kasashen da ke fama da baraka da rikice-rikice su sake hada kansu karkashin ruhin wasannin Olympics. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 

olympics
Lubabatu Lei
+ postsBio
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Yaushe Za A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza?
  • Lubabatu Lei
    https://hausa.leadership.ng/author/lubabatu-lei/
    Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Sojoji

Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.