• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

byCGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Amurka

Karin magana na harshen Hausa su kan kunshi ma’ana mai zurfi. Misali “Kome nisan jifa, kasa zai fado.” Ana amfani da wannan karin magana wajen kwatanta yanayin farawar wani batu, da faduwarsa, gami da yadda ya kai karshe a wani yanayi da ba wanda zai iya magancewa. Kan haka ne nake dora alkalamina game da labarin da na ji na rufe hukumar taimaka wa aikin raya kasashe ta Amurka (USAID) a kwanakin baya, wanda nan take ya tuna min da wannan karin magana.

A cewar gwamnatin Amurka, hukumar USAID ta gaza tabbatar da cewa ayyukan da ta ba da kudin tallafi sun dace da muradun Amurka, bayan da ta shafe shekaru 64 tana aiki. Ban da haka, sakataren harkokin waje na kasar Amurka, Marco Rubio, ya ce hukumar ba ta cimma wani abu ba face kafa dimbin kungiyoyin da ba na gwamnati ba (NGO) a duk fadin duniya. Kana a wuraren da ta shiga, ba a cika cimma burin raya kasa ba, yayin da yanayin rashin kwanciyar hankali kan ta’azzara, kuma kyamar Amurka na kara yaduwa.

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Sai dai kafin USAID ta fado kasa tamkar wani dutsen da kasar Amurka ta jefa, ta taba samun damar “tashi sama”, ma’ana cikin dogon lokaci hukumar ta zama daya daga cikin muhimman hukumomin da Amurka ke amfani da su wajen yin tasiri kan sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa, inda hukumar ta samar da kudi da karfafa kungiyoyin NGO, da kafofin watsa labaru, da cibiyoyin bincike, da dai sauransu. Kana a cikin ayyukan da USAID ta yi, har da tallafa wa cibiyar bincike dake adawa da kasar Sin ta kasar Austiraliya (ASPI), domin ta kirkira da yada jita-jita game da Sin, da ba da tallafi ga kungiyoyin NGO da ‘yan adawa na kasashen Ukraine da Georgia don kitsa sauyin mulki a kasashen. Sa’an nan, a watan Fabrairun bana, wani dan majalisar dokokin Amurka ya ce hukumar USAID ta taba samar da kudi ga kungiyoyin ‘yan ta’adda irin su Al-Qaeda, da Boko Haram ta Najeriya.

Amma a hakika, ban da wadannan miyagun abubuwa da muka ambata, USAID ita ma ta ba da wasu gudummawa, musamman ta fuskar kiwon lafiya. Misali, wani rahoton bincike da mujallar kiwon lafiya ta Birtaniya “The Lancet” ta wallafa, ya yi hasashen cewa, raguwar kudin tallafin da aka samu sakamakon rufewar USAID, na iya haddasa mutuwar mutane fiye da miliyan 14 a duniya, ciki har da yara miliyan 4.5. Amma abin takaici shi ne, a ganin gwamnatin kasar Amurka ta yau, taimaka wa dorewar rayuwar mutane a kasashe masu tasowa “ba ta dace da muradun kasar Amurka ba”.

Hakika, da ma an san cewa tabbas Amurka za ta yi watsi da USAID. Saboda kasar ta kaddamar da shirin da zai samar da cikakken tasirinta a duniya a lokacin yakin cacar baka. Amma zuwa yanzu, tauraron kasar ya riga ya fara dishewa. Don haka ta yaya za ta samu isashen karfin cimma wani tsohon burinta da ta dade da sanyawa a rai? Idan an duba kudirin dokar “Babba kuma Kyakkyawa” (big and beautiful bill) da Amurka ta zartar kwanan nan, za a ga yadda kasar ta yi shirin rage kudin tallafin aikin jinya da na abinci, da sauran kudin tabbatar da jin dadin jama’a a cikin gidanta. Ta haka mun san cewa, ba za ta ci gaba da dora muhimmanci kan aikin jin kai a kasashen ketare ba.

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Ta la’akari da wannan yanayin da kasar Amurka ke ciki, ma iya cewa, ita kanta ta zama kamar wani dutse ne da ke fadowa, kuma tabbas wata rana zai taba kasa! (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version