• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Zagon Kasa (EFCC), ta ce gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Matawalle na fuskantar bincike kan zargin almundahanar Naira biliyan 70.

Hukumar, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, ta ce ana binciken gwamnan na APC kan zargin cin hanci da rashawa, bayar da kwangiloli da kuma karkatar da sama da Naira biliyan 70.

  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka
  • Na Yi Mamakin Ganawar Antony Blinken Da Tinubu -Atiku

“Kudaden da aka samo a matsayin lamuni daga tsohon bankin da ake zargin don gudanar da ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar, ana zargin gwamnan ne ya karkatar da su ta hanyar wasu ‘yan kwangila wadanda suka karbi kudin kwangilar da ba a aiwatar da su ba.”

“Binciken da Hukumar ta gudanar ya zuwa yanzu ya nuna cewa sama da kamfanoni 100 ne suka karbi kudaden, ba tare da wata shaida ta hidimar da aka yi wa jihar ba.”

EFCC ta ce an gayyaci wasu daga cikin ‘yan kwangilar tare da yi musu tambayoyi, inda ta kara da cewa “sun bayyana bayanai kan yadda ake zargin gwamnan ya tilasta musu mayar masa da kudaden da suka karba daga asusun gwamnati ta hannun mukarrabansa bayan sun mayar da su Dalar Amurka”.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

“Sun tabbatar da cewa ba su yi wa jihar Zamfara wani aiki ba amma an ce an umarce su da su mayar da kudaden da aka biya su dalar Amurka su koma hannun gwamnan jihar ta hannun wasu kwamishinoninsa, musamman kwamishinonin da ke kula da harkokin kudi da kananan hukumomi.”

“A ci gaba da bincike kan bada kwangilar da gwamnatin Matawalle ke yi, musamman na ayyuka a kananan hukumomi, hukumar ta kwato kudi Naira miliyan 300 daga wani kamfani mai suna Fezel Nigeria Limited. An gano kudaden ne zuwa kamfanin Zamafara Investment Company.

“A Nijeriya gwamnoni da mataimakansu na da kariya daga fuskantar tuhuma yayin da suke kan mulki, dalilin da ya sa har yanzu EFCC ba ta kama Gwamna Matawalle ba ke nan.”

Matawalle, wanda ya sha kaye a zaben gwamnan jihar na 2023 a watan Maris, zai kammala wa’adin mulkinsa na shekara hudu a ranar 29 ga wata Mayu, 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaBincikeEFCCKwangilaMatawalleZamfaraZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka

Next Post

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

16 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

20 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

21 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.