• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Zagon Kasa (EFCC), ta ce gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Matawalle na fuskantar bincike kan zargin almundahanar Naira biliyan 70.

Hukumar, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, ta ce ana binciken gwamnan na APC kan zargin cin hanci da rashawa, bayar da kwangiloli da kuma karkatar da sama da Naira biliyan 70.

  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka
  • Na Yi Mamakin Ganawar Antony Blinken Da Tinubu -Atiku

“Kudaden da aka samo a matsayin lamuni daga tsohon bankin da ake zargin don gudanar da ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar, ana zargin gwamnan ne ya karkatar da su ta hanyar wasu ‘yan kwangila wadanda suka karbi kudin kwangilar da ba a aiwatar da su ba.”

“Binciken da Hukumar ta gudanar ya zuwa yanzu ya nuna cewa sama da kamfanoni 100 ne suka karbi kudaden, ba tare da wata shaida ta hidimar da aka yi wa jihar ba.”

EFCC ta ce an gayyaci wasu daga cikin ‘yan kwangilar tare da yi musu tambayoyi, inda ta kara da cewa “sun bayyana bayanai kan yadda ake zargin gwamnan ya tilasta musu mayar masa da kudaden da suka karba daga asusun gwamnati ta hannun mukarrabansa bayan sun mayar da su Dalar Amurka”.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

“Sun tabbatar da cewa ba su yi wa jihar Zamfara wani aiki ba amma an ce an umarce su da su mayar da kudaden da aka biya su dalar Amurka su koma hannun gwamnan jihar ta hannun wasu kwamishinoninsa, musamman kwamishinonin da ke kula da harkokin kudi da kananan hukumomi.”

“A ci gaba da bincike kan bada kwangilar da gwamnatin Matawalle ke yi, musamman na ayyuka a kananan hukumomi, hukumar ta kwato kudi Naira miliyan 300 daga wani kamfani mai suna Fezel Nigeria Limited. An gano kudaden ne zuwa kamfanin Zamafara Investment Company.

“A Nijeriya gwamnoni da mataimakansu na da kariya daga fuskantar tuhuma yayin da suke kan mulki, dalilin da ya sa har yanzu EFCC ba ta kama Gwamna Matawalle ba ke nan.”

Matawalle, wanda ya sha kaye a zaben gwamnan jihar na 2023 a watan Maris, zai kammala wa’adin mulkinsa na shekara hudu a ranar 29 ga wata Mayu, 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaBincikeEFCCKwangilaMatawalleZamfaraZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka

Next Post

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

Related

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin
Manyan Labarai

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

27 minutes ago
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

10 hours ago
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

15 hours ago
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
Manyan Labarai

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

20 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu
Manyan Labarai

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

21 hours ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 day ago
Next Post
NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

September 4, 2025
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.