ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70

by Sadiq
3 years ago
EFCC

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Zagon Kasa (EFCC), ta ce gwamnan Jihar Zamfara mai barin gado, Bello Matawalle na fuskantar bincike kan zargin almundahanar Naira biliyan 70.

Hukumar, a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, ta ce ana binciken gwamnan na APC kan zargin cin hanci da rashawa, bayar da kwangiloli da kuma karkatar da sama da Naira biliyan 70.

  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Kisan Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka
  • Na Yi Mamakin Ganawar Antony Blinken Da Tinubu -Atiku

“Kudaden da aka samo a matsayin lamuni daga tsohon bankin da ake zargin don gudanar da ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar, ana zargin gwamnan ne ya karkatar da su ta hanyar wasu ‘yan kwangila wadanda suka karbi kudin kwangilar da ba a aiwatar da su ba.”

ADVERTISEMENT

“Binciken da Hukumar ta gudanar ya zuwa yanzu ya nuna cewa sama da kamfanoni 100 ne suka karbi kudaden, ba tare da wata shaida ta hidimar da aka yi wa jihar ba.”

EFCC ta ce an gayyaci wasu daga cikin ‘yan kwangilar tare da yi musu tambayoyi, inda ta kara da cewa “sun bayyana bayanai kan yadda ake zargin gwamnan ya tilasta musu mayar masa da kudaden da suka karba daga asusun gwamnati ta hannun mukarrabansa bayan sun mayar da su Dalar Amurka”.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

“Sun tabbatar da cewa ba su yi wa jihar Zamfara wani aiki ba amma an ce an umarce su da su mayar da kudaden da aka biya su dalar Amurka su koma hannun gwamnan jihar ta hannun wasu kwamishinoninsa, musamman kwamishinonin da ke kula da harkokin kudi da kananan hukumomi.”

“A ci gaba da bincike kan bada kwangilar da gwamnatin Matawalle ke yi, musamman na ayyuka a kananan hukumomi, hukumar ta kwato kudi Naira miliyan 300 daga wani kamfani mai suna Fezel Nigeria Limited. An gano kudaden ne zuwa kamfanin Zamafara Investment Company.

“A Nijeriya gwamnoni da mataimakansu na da kariya daga fuskantar tuhuma yayin da suke kan mulki, dalilin da ya sa har yanzu EFCC ba ta kama Gwamna Matawalle ba ke nan.”

Matawalle, wanda ya sha kaye a zaben gwamnan jihar na 2023 a watan Maris, zai kammala wa’adin mulkinsa na shekara hudu a ranar 29 ga wata Mayu, 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.