• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai bai wa shugaban kasa shawara ta fannin bunkasa zamantakewa, Miss Maryam Uwais ta bayyana cewa sakamakon karuwar yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya ya sa gwamnatin tarayya ta bullo da shirin tsamo yara daga hatsari (ARC-P).

Wannan shiri ne da zai magance matsalar da yara da kuma matasa suke fuskanta a dukkanin jihohin kasar nan ciki har da Babban Birnin Tarayya.

  • Mahara Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Wani Hari Da Suka Kai Enugu
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Kwalejin Nazarin Kide-Kide Na Princess Galyani Vadana

Da take jawabi a wurin taron kara wa juna sani na kwanaki uku da za a horar da matasa har sama da 900 a Maiduguri da ke Jihar Borno, Misis Maryam wacce ta kasance jagorar shirin karkashin ofishin mataimakin shugaban kasa, ta bayyana cewa an samar da wannan shirin ne domin magance matsalolin da ke addabar yara da kuma matasa a fadin Nijeriya, wajen yin amfani da wasu matakai da suke da alaka da ilimi da lafiya da horar da sana’o’in da noma da kuwa wasanni.

Misis Maryam wadda ta samu wakilcin mataimakin daraktar kasafi da tsare-tsare, Grace Akpabio ta ce za a gudanar da bayar da horon ga matasa a Jihar Borno har na tsawan makonni uku, domin samar musu da sana’o’in dogaro da kai.

A cewar mashawarciyar shugaban kasan, horar zai bunkasa basirar matasan wanda zai yi daidai da shirin ARC-P wajen tallafa wa rayuwarsu da kuma al’umma. Ta kara da cewa matasan da za su amfana da shirin suna da matukar rawar da za su taka wajen cimma nasarar wannan shirin wanda gwamnatin tarayya ta kaddamar tare da tallafin bangaren ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

A nasa jawarin, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya yaba wa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin APC na samar da shirin ARC-P. Ya ce a yanzu haka shirin yana gudana a kasa wanda zai shafe shekaru 25 yana gudana.

Zulum wanda ya samu wakilcin kwamishinan harkokin mata, Hajiya Zuwaira Gambo ya ce gwamnatin tarayya ta samar da shirye-shirye kamar irinsu ARC-P wadanda za su taimaka wajen magance matsalolin yara da matasa da mata musamman a yankin arewa maso yamma da yakin Boko Haram ya daidaita a tsawan shekari 12 da suka gabata.

Gwamna Zulum ya sha alwashin hada kai da tawagar shirin ARC-P wajen bayar da goyon baya domin shirin ya samu nasara, yayin da kuma ya yi kira ga matasan su jajirce wajen ganin sun amfanar da rayuwarsu kan wannan shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BulloFadar Shugaban KasaMakarantaShiriYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Akwai Yiwuwar Zagaye Na Biyu Idan Zaben Shugaban Kasa Bai Fitar Da Dan Takara Ba – INEC

Next Post

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

16 minutes ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

12 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

12 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

14 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

17 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

17 hours ago
Next Post
FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.