• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai bai wa shugaban kasa shawara ta fannin bunkasa zamantakewa, Miss Maryam Uwais ta bayyana cewa sakamakon karuwar yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya ya sa gwamnatin tarayya ta bullo da shirin tsamo yara daga hatsari (ARC-P).

Wannan shiri ne da zai magance matsalar da yara da kuma matasa suke fuskanta a dukkanin jihohin kasar nan ciki har da Babban Birnin Tarayya.

  • Mahara Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Wani Hari Da Suka Kai Enugu
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Kwalejin Nazarin Kide-Kide Na Princess Galyani Vadana

Da take jawabi a wurin taron kara wa juna sani na kwanaki uku da za a horar da matasa har sama da 900 a Maiduguri da ke Jihar Borno, Misis Maryam wacce ta kasance jagorar shirin karkashin ofishin mataimakin shugaban kasa, ta bayyana cewa an samar da wannan shirin ne domin magance matsalolin da ke addabar yara da kuma matasa a fadin Nijeriya, wajen yin amfani da wasu matakai da suke da alaka da ilimi da lafiya da horar da sana’o’in da noma da kuwa wasanni.

Misis Maryam wadda ta samu wakilcin mataimakin daraktar kasafi da tsare-tsare, Grace Akpabio ta ce za a gudanar da bayar da horon ga matasa a Jihar Borno har na tsawan makonni uku, domin samar musu da sana’o’in dogaro da kai.

A cewar mashawarciyar shugaban kasan, horar zai bunkasa basirar matasan wanda zai yi daidai da shirin ARC-P wajen tallafa wa rayuwarsu da kuma al’umma. Ta kara da cewa matasan da za su amfana da shirin suna da matukar rawar da za su taka wajen cimma nasarar wannan shirin wanda gwamnatin tarayya ta kaddamar tare da tallafin bangaren ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

Labarai Masu Nasaba

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

A nasa jawarin, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya yaba wa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin APC na samar da shirin ARC-P. Ya ce a yanzu haka shirin yana gudana a kasa wanda zai shafe shekaru 25 yana gudana.

Zulum wanda ya samu wakilcin kwamishinan harkokin mata, Hajiya Zuwaira Gambo ya ce gwamnatin tarayya ta samar da shirye-shirye kamar irinsu ARC-P wadanda za su taimaka wajen magance matsalolin yara da matasa da mata musamman a yankin arewa maso yamma da yakin Boko Haram ya daidaita a tsawan shekari 12 da suka gabata.

Gwamna Zulum ya sha alwashin hada kai da tawagar shirin ARC-P wajen bayar da goyon baya domin shirin ya samu nasara, yayin da kuma ya yi kira ga matasan su jajirce wajen ganin sun amfanar da rayuwarsu kan wannan shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BulloFadar Shugaban KasaMakarantaShiriYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Akwai Yiwuwar Zagaye Na Biyu Idan Zaben Shugaban Kasa Bai Fitar Da Dan Takara Ba – INEC

Next Post

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

Related

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

40 minutes ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

12 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

13 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

14 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

17 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

19 hours ago
Next Post
FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

LABARAI MASU NASABA

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.