• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin Ta Taruka Biyu Na Kasar

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Fahimtar Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin Ta Taruka Biyu Na Kasar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan taruka biyu na kasar Sin sun sa duniya ta fara tunanin “Shin mene ne ma’anar Demokuradiyya”. A ra’ayin babban editan mujallar “Dang Dai” ta kasar Argentina, Gustavo Ng, tsarin demokuradiyyar kasar Sin dake mayar da hankali kan jama’a ta kowacce fuska, ita ce Demokuradiyyar da jama’a suke amfana da ita. A cewarsa, manyan taruka biyu da ake gudanarwa shekara-shekara, wata muhimmiyar taga ce da duniya za ta iya lura tare da fahimtar tsarin demokuradiyya dake mayar da hankali kan jama’a ta kowacce fuska.

Sun Jie, mambar Majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC daga Beijing, ta gabatar da wasu shawarwari a yayin tarukan biyu na bana, wadanda suke mayar da hankali kan inganta tsarin tallafin abinci ga wadanda suka manyanta da kara kyautata al’ummar dake mayar da hankali kan tsoffi. A bara, Sun Jie ta mika dubban takardun tambayoyi ga jama’a da gudanar da bincike a yankuna da kuma shirya tarukan karawa juna sani, domin tabbatar da shawararta ta bayyana ainihin matsalar dake akwai.

  • Shugaban Sin Ya Taya Asif Ali Zardari Murnar Lashe Zaben Shugaban Pakistan
  • CPPCC Ya Rufe Cikakken Taronsa Na Shekara-shekara 

Kusan wakilai 3,000 na Majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC da sama da mambobi 2,100 na Majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC daga dukkan fadin kasar ne suka hadu a Beijing, tafe da muryoyin jama’a zuwa dandalin mafi muhimmanci domin a dama da su cikin ayyukan tattauna batutuwan kasa, da bayar da shawarwari domin ci gaban kasar, lamarin dake kara nunawa duniya irin kuzarin da tsarin demokuradiyyar kasar Sin ke da shi.

Demokuradiyya ba ado ba ne, bai kamata a rika amfani da ita kamar kayan ado ba, sai dai don ta warware matsalolin da jama’a suke fuskanta. Bisa kididdiga, a bara, sassa da dama na majalisar gudanarwa ta kasar Sin, sun karbi shawarwari sama da 12,000 da aka gabatar yayin manyan tarukan biyu, kuma an kammala nazartarsu a kan lokaci. Sassan sun amince da kusan ra’ayoyi da shawarwari 4,700 da wakilan jama’a na majalisar NPC da mambobin majalisar CPPCC suka gabatar, tare da kaddamar da sama da matakai da manufofi fiye da 2,000 wadanda suka inganta ci gaban tattalin arziki da ma rayuwar jama’ar kasar.

Ta wadannan taruka 2, duniya za ta iya fahimtar tsarin demokuradiyya irin na kasar Sin da fahimtar fa’idojinsa da ma tsarin ci gaban kasar. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Kaddamar Da Shirin Bayar Da Lamunin Dalibai A Ranar Alhamis

Next Post

Ramadan: Gwamnatin Sokoto Ta Amince A Biya Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Kyautar Rabin Albashi

Related

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
Daga Birnin Sin

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

3 minutes ago
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

7 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

9 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

10 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

21 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

22 hours ago
Next Post
Ramadan: Gwamnatin Sokoto Ta Amince A Biya Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Kyautar Rabin Albashi

Ramadan: Gwamnatin Sokoto Ta Amince A Biya Ma'aikata Da 'Yan Fansho Kyautar Rabin Albashi

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.