ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fahimtar Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin Ta Taruka Biyu Na Kasar

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Manyan taruka biyu na kasar Sin sun sa duniya ta fara tunanin “Shin mene ne ma’anar Demokuradiyya”. A ra’ayin babban editan mujallar “Dang Dai” ta kasar Argentina, Gustavo Ng, tsarin demokuradiyyar kasar Sin dake mayar da hankali kan jama’a ta kowacce fuska, ita ce Demokuradiyyar da jama’a suke amfana da ita. A cewarsa, manyan taruka biyu da ake gudanarwa shekara-shekara, wata muhimmiyar taga ce da duniya za ta iya lura tare da fahimtar tsarin demokuradiyya dake mayar da hankali kan jama’a ta kowacce fuska.

Sun Jie, mambar Majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC daga Beijing, ta gabatar da wasu shawarwari a yayin tarukan biyu na bana, wadanda suke mayar da hankali kan inganta tsarin tallafin abinci ga wadanda suka manyanta da kara kyautata al’ummar dake mayar da hankali kan tsoffi. A bara, Sun Jie ta mika dubban takardun tambayoyi ga jama’a da gudanar da bincike a yankuna da kuma shirya tarukan karawa juna sani, domin tabbatar da shawararta ta bayyana ainihin matsalar dake akwai.

  • Shugaban Sin Ya Taya Asif Ali Zardari Murnar Lashe Zaben Shugaban Pakistan
  • CPPCC Ya Rufe Cikakken Taronsa Na Shekara-shekara 

Kusan wakilai 3,000 na Majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC da sama da mambobi 2,100 na Majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC daga dukkan fadin kasar ne suka hadu a Beijing, tafe da muryoyin jama’a zuwa dandalin mafi muhimmanci domin a dama da su cikin ayyukan tattauna batutuwan kasa, da bayar da shawarwari domin ci gaban kasar, lamarin dake kara nunawa duniya irin kuzarin da tsarin demokuradiyyar kasar Sin ke da shi.

ADVERTISEMENT

Demokuradiyya ba ado ba ne, bai kamata a rika amfani da ita kamar kayan ado ba, sai dai don ta warware matsalolin da jama’a suke fuskanta. Bisa kididdiga, a bara, sassa da dama na majalisar gudanarwa ta kasar Sin, sun karbi shawarwari sama da 12,000 da aka gabatar yayin manyan tarukan biyu, kuma an kammala nazartarsu a kan lokaci. Sassan sun amince da kusan ra’ayoyi da shawarwari 4,700 da wakilan jama’a na majalisar NPC da mambobin majalisar CPPCC suka gabatar, tare da kaddamar da sama da matakai da manufofi fiye da 2,000 wadanda suka inganta ci gaban tattalin arziki da ma rayuwar jama’ar kasar.

Ta wadannan taruka 2, duniya za ta iya fahimtar tsarin demokuradiyya irin na kasar Sin da fahimtar fa’idojinsa da ma tsarin ci gaban kasar. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamnatin Sokoto Ta Amince A Biya Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Kyautar Rabin Albashi

Ramadan: Gwamnatin Sokoto Ta Amince A Biya Ma'aikata Da 'Yan Fansho Kyautar Rabin Albashi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.