• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]

by Nuhu Ubale Ibrahim
7 months ago
in Labarai
0
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَالحَاسِدُ يَضُرُّ نَفْسَهُ ثَلَاثَ مَضَرَّاتٍ: أَحَدُهَا اكْتِسَابُ الذُّنُوبِ، لِأَنَّ الحَسَدَ حَرَامٌ. الثَّانِيَةُ سُوءُ الأَدَبِ مَعَ اللهِ، فَإِنَّ حَقِيقَةَ الحَسَدِ كَرَاهِيَةُ إِنْعَامِ اللهِ عَلَى عَبْدِهِ، وَاعْتِرَاضٌ عَلَى اللهِ فِي فِعْلِهِ. الثَّالِثَةُ تَأَلُّمُ قَلْبِهِ مِنْ كَثْرَةِ هَمِّهِ وَغَمِّهِ.

Fassara:

“Mai hassada yana cutar da kansa ta hanyoyi guda uku:

● Ta farko, yana tarawa kansa zunubi, domin hassada haramun ce.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

● Ta biyu, yana nuna rashin ladabi ga Allah, domin ainihin hassada ita ce jin haushin yadda Allah Ya ba wa wani ni’ima, kuma hakan yana nufin yana sukar hukuncin Allah.

● Ta uku, zuciyarsa tana shan wahala saboda yawan damuwa da baƙin ciki.”

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai Allah Ya ji ƙan sa, ya yi cikakken bayani kan illolin hassada ga mai hassada ta hanyoyi guda uku: samun zunubi, da rashin ladabi ga Allah, da wahalar da zuciya.

Zan ɗan yi bayani a kan waɗan gaɓoɓi guda uku da malam ya ambata, tare da hujjoji daga Alƙur’ani, da Hadisi, da mahangar masana ilimi. Ga maganar kamar haka:

Hassada Zunubi Ce Kuma Haramun Ce a Shari’a:

A Musulunci, hassada tana daga cikin manyan zunubai. Dalili kuwa shi ne cewa tana ƙunshe da ƙiyayya da kishi mara dalili. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:” Shin yanzu za su riƙa yi wa mutane hassada ne a kan abin da Allah Ya ba su na falalarsa?” Suratun Nisã’i aya ta 54. Ma’anar wannan aya ita ce: idan mutum yana jin haushin wani saboda wata ni’ima da Allah Ya ba shi, to yana fuskantar hukuncin Allah da kishi maras tushe. Haka nan Annabi (SAW) ya fadi a cikin hadisi cewa: “Kada ku yi hassada“ Bukhari da Muslim ne ya ruwaito.

Me Yasa Hassada Take Zama Zunubi?

Hassada ta zama zunubi ne ta fuskoki masu yawa.

• Akwai saɓa wa Allah da Manzonsa (S.A.W) na hani a kan hassada.
• Hassada tana sa mutum ya yi mummunan zato ga Allah, yana ganin kamar bai dace Allah Ya ba wani wata ni’ima ba.
• Hassada tana iya sa mutum ya aikata mugun aiki, kamar cutar da wanda yake yi wa hassada.
• Hassada tana hana mutum mai da hankali kan nasararsa, tare da an giza shi yana riƙa jin haushin wasu maimakon yin aikin da zai amfane shi.
• Hassada tana hana mutum gode wa Allah da abin da yake da shi.

Mafita:
Maimakon haka, Musulunci ya na koyar da yin gibḍa (kishi mai kyau), wato yin burin yin abin da wani yake yi ba tare da fatan sharri gare shi ba. Misali, idan mutum yana ganin wani ya fi shi ilimi, maimakon yin hassada, yana da kyau ya yi addu’a Allah Ya ba shi ilimi kamar nasa.

Hassada Rashin Ladabi Ce Ga Allah:

Idan mutum yana jin haushin yadda wani ya samu wata ni’ima, hakan yana nufin yana ƙin hukuncin Allah ne. Wannan kuwa yana iya jefa mutum cikin shakka ko rashin yarda da Allah. Allah Ta’ala Ya ce a cikin Alƙur’ani: ”Kuma Allah Yana bayar da mulkinsa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai Yalwa ne, Masani” Suratul Baƙara aya ta 247.

A ma’anar wannan aya ita ce, Allah ne yake rarraba arziki, da ilimi, da kyau, da sauran ni’imomi ga wanda Ya ga dama. Idan mutum yana jin haushin wannan, to yana sukar hukuncin Allah ne. Misali a rayuwa, Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da dukiya, wannan yana nuna cewa bai gamsu da yadda Allah ke bayar da arziki ba. Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da kyau ko hikima, yana nufin yana ƙin tsarin Allah ne. Hassada tana sa mutum ya yi tambayoyi marasa amfani, kamar:

○ Me yasa Allah Ya ba wane, amma ni bai ba ni ba?”
○ Me yasa ni ban samu kaza ba alhali na fi shi ƙoƙari?
Waɗannan tunani suna iya jefa mutum cikin gaba da ƙaddara, wanda hakan yana daga cikin munanan al’amura a Musulunci da suke taɓa imanin bawa.

Hassada Tana Jefa Mai Yi Cikin Wahalar Zuciya da Damuwa:

Baya ga kasancewar hassada zunubi, hassada tana cutar da zuciyar mai yi. Wannan yana da nasaba da ilimin halayyar dan ɗan’adam (wato psychology), wanda ya tabbatar da cewa hassada tana jefa mutum cikin damuwa da ciwon zuciya.

Yadda Hassada Take Hana Jin Daɗi:

Hassada tana hana mai hassada jin daɗi ta fuskoki masu yawa da suka haɗa da:

● Mai hassada yana rayuwa cikin baƙin ciki, saboda yana kallon wasu yana jin haushinsu.
Yana cike da damuwa, saboda yana son a cire wa wani wata ni’ima a maimakon ya mai da hankali kan kansa.
● Mai hassada yana ƙin farin cikin wasu, idan wani ya yi nasara, sai ya ji haushi a maimakon ya taya su murna.

Ga Wa su Misali a Rayuwa:
1. Idan mutum yana jin haushin wani saboda ya sami aiki, yana iya shafe kwanaki yana tunanin hakan a maimakon neman na kansa.
2. Idan mutum yana jin haushin abokin karatunsa saboda ya fi shi kyau, yana iya jin ƙunci da matsin lamba a maimakon ƙoƙarin kyautata halinsa. Allah Ya tsare mu daga hassada, Ya sa mu kasance cikin masu gode Masa da kyawawan halaye! Amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abu Razina Nuhu Ubale PakiAl-qur'aniAlƙur’aniIbnu JuzaiRamadanTafsiriTafsirin Alƙur’aniTafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi

Next Post

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

24 hours ago
Next Post
Tinubu

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.