ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya yi masa rahama yana cewa:

وَالحَاسِدُ يَضُرُّ نَفْسَهُ ثَلَاثَ مَضَرَّاتٍ: أَحَدُهَا اكْتِسَابُ الذُّنُوبِ، لِأَنَّ الحَسَدَ حَرَامٌ. الثَّانِيَةُ سُوءُ الأَدَبِ مَعَ اللهِ، فَإِنَّ حَقِيقَةَ الحَسَدِ كَرَاهِيَةُ إِنْعَامِ اللهِ عَلَى عَبْدِهِ، وَاعْتِرَاضٌ عَلَى اللهِ فِي فِعْلِهِ. الثَّالِثَةُ تَأَلُّمُ قَلْبِهِ مِنْ كَثْرَةِ هَمِّهِ وَغَمِّهِ.

Fassara:

ADVERTISEMENT

“Mai hassada yana cutar da kansa ta hanyoyi guda uku:

● Ta farko, yana tarawa kansa zunubi, domin hassada haramun ce.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

● Ta biyu, yana nuna rashin ladabi ga Allah, domin ainihin hassada ita ce jin haushin yadda Allah Ya ba wa wani ni’ima, kuma hakan yana nufin yana sukar hukuncin Allah.

● Ta uku, zuciyarsa tana shan wahala saboda yawan damuwa da baƙin ciki.”

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Fashin Baƙi:

Ibn Juzai Allah Ya ji ƙan sa, ya yi cikakken bayani kan illolin hassada ga mai hassada ta hanyoyi guda uku: samun zunubi, da rashin ladabi ga Allah, da wahalar da zuciya.

Zan ɗan yi bayani a kan waɗan gaɓoɓi guda uku da malam ya ambata, tare da hujjoji daga Alƙur’ani, da Hadisi, da mahangar masana ilimi. Ga maganar kamar haka:

Hassada Zunubi Ce Kuma Haramun Ce a Shari’a:

A Musulunci, hassada tana daga cikin manyan zunubai. Dalili kuwa shi ne cewa tana ƙunshe da ƙiyayya da kishi mara dalili. Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:” Shin yanzu za su riƙa yi wa mutane hassada ne a kan abin da Allah Ya ba su na falalarsa?” Suratun Nisã’i aya ta 54. Ma’anar wannan aya ita ce: idan mutum yana jin haushin wani saboda wata ni’ima da Allah Ya ba shi, to yana fuskantar hukuncin Allah da kishi maras tushe. Haka nan Annabi (SAW) ya fadi a cikin hadisi cewa: “Kada ku yi hassada“ Bukhari da Muslim ne ya ruwaito.

Me Yasa Hassada Take Zama Zunubi?

Hassada ta zama zunubi ne ta fuskoki masu yawa.

• Akwai saɓa wa Allah da Manzonsa (S.A.W) na hani a kan hassada.
• Hassada tana sa mutum ya yi mummunan zato ga Allah, yana ganin kamar bai dace Allah Ya ba wani wata ni’ima ba.
• Hassada tana iya sa mutum ya aikata mugun aiki, kamar cutar da wanda yake yi wa hassada.
• Hassada tana hana mutum mai da hankali kan nasararsa, tare da an giza shi yana riƙa jin haushin wasu maimakon yin aikin da zai amfane shi.
• Hassada tana hana mutum gode wa Allah da abin da yake da shi.

Mafita:
Maimakon haka, Musulunci ya na koyar da yin gibḍa (kishi mai kyau), wato yin burin yin abin da wani yake yi ba tare da fatan sharri gare shi ba. Misali, idan mutum yana ganin wani ya fi shi ilimi, maimakon yin hassada, yana da kyau ya yi addu’a Allah Ya ba shi ilimi kamar nasa.

Hassada Rashin Ladabi Ce Ga Allah:

Idan mutum yana jin haushin yadda wani ya samu wata ni’ima, hakan yana nufin yana ƙin hukuncin Allah ne. Wannan kuwa yana iya jefa mutum cikin shakka ko rashin yarda da Allah. Allah Ta’ala Ya ce a cikin Alƙur’ani: ”Kuma Allah Yana bayar da mulkinsa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai Yalwa ne, Masani” Suratul Baƙara aya ta 247.

A ma’anar wannan aya ita ce, Allah ne yake rarraba arziki, da ilimi, da kyau, da sauran ni’imomi ga wanda Ya ga dama. Idan mutum yana jin haushin wannan, to yana sukar hukuncin Allah ne. Misali a rayuwa, Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da dukiya, wannan yana nuna cewa bai gamsu da yadda Allah ke bayar da arziki ba. Idan mutum yana jin haushin wani saboda yana da kyau ko hikima, yana nufin yana ƙin tsarin Allah ne. Hassada tana sa mutum ya yi tambayoyi marasa amfani, kamar:

○ Me yasa Allah Ya ba wane, amma ni bai ba ni ba?”
○ Me yasa ni ban samu kaza ba alhali na fi shi ƙoƙari?
Waɗannan tunani suna iya jefa mutum cikin gaba da ƙaddara, wanda hakan yana daga cikin munanan al’amura a Musulunci da suke taɓa imanin bawa.

Hassada Tana Jefa Mai Yi Cikin Wahalar Zuciya da Damuwa:

Baya ga kasancewar hassada zunubi, hassada tana cutar da zuciyar mai yi. Wannan yana da nasaba da ilimin halayyar dan ɗan’adam (wato psychology), wanda ya tabbatar da cewa hassada tana jefa mutum cikin damuwa da ciwon zuciya.

Yadda Hassada Take Hana Jin Daɗi:

Hassada tana hana mai hassada jin daɗi ta fuskoki masu yawa da suka haɗa da:

● Mai hassada yana rayuwa cikin baƙin ciki, saboda yana kallon wasu yana jin haushinsu.
Yana cike da damuwa, saboda yana son a cire wa wani wata ni’ima a maimakon ya mai da hankali kan kansa.
● Mai hassada yana ƙin farin cikin wasu, idan wani ya yi nasara, sai ya ji haushi a maimakon ya taya su murna.

Ga Wa su Misali a Rayuwa:
1. Idan mutum yana jin haushin wani saboda ya sami aiki, yana iya shafe kwanaki yana tunanin hakan a maimakon neman na kansa.
2. Idan mutum yana jin haushin abokin karatunsa saboda ya fi shi kyau, yana iya jin ƙunci da matsin lamba a maimakon ƙoƙarin kyautata halinsa. Allah Ya tsare mu daga hassada, Ya sa mu kasance cikin masu gode Masa da kyawawan halaye! Amin.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Tinubu

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.