• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]

byNuhu Ubale Ibrahim
7 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Rabe-raben Hassada:

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana cewa:

إِنَّ الحَسَدَ عَلَى دَرَجَاتٍ: الأُولَى أَنْ يُحِبَّ الإِنْسَانُ زَوَالَ النِّعْمَةِ عَنْ أَخِيهِ المُسْلِمِ وَإِنْ كَانَتْ لَا تَنْتَقِلُ إِلَيْهِ، بَلْ يَكْرَهُ إِنْعَامَ اللَّهِ عَلَى غَيْرِهِ وَيَتَأَلَّمُ بِهِ. الثَّانِيَةُ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَ تِلْكَ النِّعْمَةِ لِرَغْبَتِهِ فِيهَا، رَجَاءَ انْتِقَالِهَا إِلَيْهِ. الثَّالِثَةُ أَنْ يَتَمَنَّى لِنَفْسِهِ مِثْلَ تِلْكَ النِّعْمَةِ مِنْ غَيْرِ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَهَا عَنْ غَيْرِهِ، وَهَذَا جَائِزٌ وَلَيْسَ بِحَسَدٍ، وَإِنَّمَا هُوَ غِبْطَةٌ.

Fassara:
“ Tabbas hassada tana da matakai: Matakin farko shi ne mutum ya so ni’imar da ke hannun ɗan’uwansa musulmi ta gushe, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Sai kawai ya kyamaci ganin wani a cikin ni’imar Allah, ya ji zafin samun wannan ni’ima a hannun wani.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

Mataki na biyu shi ne mutum ya so wannan ni’ima ta gushe daga hannun wani saboda yana son ta koma gare shi, saboda kwaɗayinta da fatan amfana da ita.

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Mataki na uku shi ne mutum ya so samun irin wannan ni’ima kamar yadda wani yake da ita, ba tare da yana so ta gushe daga hannun wanda yake da ita ba. Wannan kuwa ba hassada ba ce, sai dai ana kiranta da fatan alheri ga kai.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

Fashin Baƙi:
Ibn Juzai al-Kalbi ya bayyana mana rabe-raben hassada. Inda ya ce:
● Matakin Farko na Hassada:
Shi ne mutum ya so wata ni’ima da Allah Ya ba wa wani ta gushe daga gare shi, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Wannan shi ne mafi munin nau’in hassada gaba ɗaya, kuma yana ɗaya daga cikin manyan cututtukan zuciya da ke hana albarka a rayuwa.

Wannan nau’in hassada yana nufin mutum yana jin haushin samun wata ni’ima a hannun wani, ba don yana son ita ta koma gare shi ba, sai dai kawai ya ƙi ganin wani yana da ita. Wannan yana iya kasancewa a cikin kowace irin ni’ima, kamar:
• Dukiya da arziki
• Matsayi ko shugabanci
• Ilimi da hikima
• Kyakkyawar rayuwa
Farin ciki da kwanciyar hankali da sauran su.
A wasu lokuta, mai irin wannan hassadar ba shi da watbuƙata a kan ni’imar da yake hassada, amma kawai yana jin cewa wannan mutumin bai cancanci wannan alheri ba. Wannan yana nuna kyashi da mugunta a zuciyar mai hassadar.

Alamomin Wannan Hassada:
Jin haushin duk wani alheri da wani ya samu.
Ƙin fatan wani ya cigaba ko ya sami wadata ko farin ciki. Idan ya ga wani yana cikin alheri, yana jin haushin hakan. Idan wannan ni’ima ta gushe daga hannun mai ita, sai ya ji daɗi. Baya iya ɓoye jin haushinsa idan wani ya sami nasara ko farin ciki.
Misalan Irin Wannan Hassada:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (AS): Labarin farko da ya nuna irin wannan hassadar shi ne na Iblis da Annabi Adam (AS). Allah Ya ba Adam matsayi na musamman, amma Iblis ya ƙi yarda, yana jin haushin Allah Ya ba wa Adam daraja. Bai so ya zama kamar annabi Adam (AS), sai dai kawai ya ƙi ganin annabi Adam yana da wannan matsayi har yana cewa:” Yanzu na yi sujjada ga wanda Ka halitta da taɓo?” Suratul Isrã’i aya ta 61. Iblis bai buƙaci wannan matsayi ya koma gare shi ba, amma bai son annabi Adam (AS) ya ci gaba da kasancewa a ciki ba. Wannan ita ce hassada mafi muni.

2. Hassadar Yahudawa ga Musulumi:
A cikin suratul-Baƙara, Allah Ya bayyana cewa Yahudawa sun yi hassada ga Musulumi saboda Allah Ya ba su addinin da ya fi na su. Sun san gaskiya, amma sai suka ƙi amincewa da ita saboda hassada. Allah Ta’ala Ya ce:” Da yawa daga ma’abota littafi sun yi burin jna ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su.” Suratul-Baƙara aya ta 109.

Ba don Yahudawa suna son addinin Musulunci ya kasance nasu ba, sai dai kawai suna jin haushin Musulumai sun samu wannan ni’ima.

3. Hassadar ‘Yan’uwan Annabi Yusuf (AS):
‘Yan’uwan Annabi Yusuf sun yi hassada a kansa ba don suna son su zama Annabawa ba, sai dai kawai sun ƙi ganin mahaifinsu yana ƙaunarsa fiye da su. Saboda haka, suka nemi hanyar raba shi da wannan ni’ima. Allah Yana cewa:” Ka tuna lokacin da ‘yan’uwan suka ce:” Lalle Yusufu da ɗan’uwansa babammu ya fi son su da mu, ga mu kuwa jama’a masu yawa. Lalle babammu yana cikin kuskure mabayyani.” Suratu Yusuf aya ta 8.

Suna ƙyamar ganin annabi Yusuf yana cikin soyayyar mahaifinsu, har suka yi ƙoƙarin halaka shi. Wannan yana nuna yadda hassada take kai mutum ga zalunci da cutar da wasu.

4. Illolin Wannan Hassara:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Wannan nau’in hassada yana nuna cewa mutum bai yarda da yadda Allah Yake rabon ni’ima ba. Mai irin wannan hali yana ƙin hikimar Allah da yadda Ya tsara rayuwa.

Rashin Farin Ciki da Kwanciyar Hankali: Mutum mai irin wannan hassada yana cikin damuwa a koyaushe. Yana ƙunci idan ya ga wani cikin alheri, yana fushi idan wani ya sami nasara, kuma yana jin baƙin ciki idan wani yana da wadata.

Yana Haifar da Gaba da Ƙiyayya a Tsakanin Mutane: Hassada tana haddasa gaba da ƙiyayya a tsakanin mutane. Mai irin wannan hali baya son ci gaban wasu, wanda hakan ke haifar da matsaloli a cikin al’umma.
Rashin Albarka a Rayuwa: Mutumin da yake da irin wannan hassadar ba ya samun albarka a rayuwarsa, domin Allah ba Ya albarkantar da zuciya mai kyashi da mugunta.

Allah Ya yi mana katangar ƙarfe da hasaada. Amin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’

Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa'

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version