ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Rabe-raben Hassada:

Ibnu Juzai a-Kalbi Allah Ya ji ƙan sa yana cewa:

إِنَّ الحَسَدَ عَلَى دَرَجَاتٍ: الأُولَى أَنْ يُحِبَّ الإِنْسَانُ زَوَالَ النِّعْمَةِ عَنْ أَخِيهِ المُسْلِمِ وَإِنْ كَانَتْ لَا تَنْتَقِلُ إِلَيْهِ، بَلْ يَكْرَهُ إِنْعَامَ اللَّهِ عَلَى غَيْرِهِ وَيَتَأَلَّمُ بِهِ. الثَّانِيَةُ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَ تِلْكَ النِّعْمَةِ لِرَغْبَتِهِ فِيهَا، رَجَاءَ انْتِقَالِهَا إِلَيْهِ. الثَّالِثَةُ أَنْ يَتَمَنَّى لِنَفْسِهِ مِثْلَ تِلْكَ النِّعْمَةِ مِنْ غَيْرِ أَنْ يُحِبَّ زَوَالَهَا عَنْ غَيْرِهِ، وَهَذَا جَائِزٌ وَلَيْسَ بِحَسَدٍ، وَإِنَّمَا هُوَ غِبْطَةٌ.

ADVERTISEMENT

Fassara:
“ Tabbas hassada tana da matakai: Matakin farko shi ne mutum ya so ni’imar da ke hannun ɗan’uwansa musulmi ta gushe, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Sai kawai ya kyamaci ganin wani a cikin ni’imar Allah, ya ji zafin samun wannan ni’ima a hannun wani.

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [14]

Mataki na biyu shi ne mutum ya so wannan ni’ima ta gushe daga hannun wani saboda yana son ta koma gare shi, saboda kwaɗayinta da fatan amfana da ita.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Mataki na uku shi ne mutum ya so samun irin wannan ni’ima kamar yadda wani yake da ita, ba tare da yana so ta gushe daga hannun wanda yake da ita ba. Wannan kuwa ba hassada ba ce, sai dai ana kiranta da fatan alheri ga kai.” Duba Kitãbu at-Tashīlu Li’ulūmi at-Tanzil [4/226]

Fashin Baƙi:
Ibn Juzai al-Kalbi ya bayyana mana rabe-raben hassada. Inda ya ce:
● Matakin Farko na Hassada:
Shi ne mutum ya so wata ni’ima da Allah Ya ba wa wani ta gushe daga gare shi, ko da kuwa ba zai amfana da ita ba. Wannan shi ne mafi munin nau’in hassada gaba ɗaya, kuma yana ɗaya daga cikin manyan cututtukan zuciya da ke hana albarka a rayuwa.

Wannan nau’in hassada yana nufin mutum yana jin haushin samun wata ni’ima a hannun wani, ba don yana son ita ta koma gare shi ba, sai dai kawai ya ƙi ganin wani yana da ita. Wannan yana iya kasancewa a cikin kowace irin ni’ima, kamar:
• Dukiya da arziki
• Matsayi ko shugabanci
• Ilimi da hikima
• Kyakkyawar rayuwa
Farin ciki da kwanciyar hankali da sauran su.
A wasu lokuta, mai irin wannan hassadar ba shi da watbuƙata a kan ni’imar da yake hassada, amma kawai yana jin cewa wannan mutumin bai cancanci wannan alheri ba. Wannan yana nuna kyashi da mugunta a zuciyar mai hassadar.

Alamomin Wannan Hassada:
Jin haushin duk wani alheri da wani ya samu.
Ƙin fatan wani ya cigaba ko ya sami wadata ko farin ciki. Idan ya ga wani yana cikin alheri, yana jin haushin hakan. Idan wannan ni’ima ta gushe daga hannun mai ita, sai ya ji daɗi. Baya iya ɓoye jin haushinsa idan wani ya sami nasara ko farin ciki.
Misalan Irin Wannan Hassada:

1. Hassadar Iblis ga Annabi Adam (AS): Labarin farko da ya nuna irin wannan hassadar shi ne na Iblis da Annabi Adam (AS). Allah Ya ba Adam matsayi na musamman, amma Iblis ya ƙi yarda, yana jin haushin Allah Ya ba wa Adam daraja. Bai so ya zama kamar annabi Adam (AS), sai dai kawai ya ƙi ganin annabi Adam yana da wannan matsayi har yana cewa:” Yanzu na yi sujjada ga wanda Ka halitta da taɓo?” Suratul Isrã’i aya ta 61. Iblis bai buƙaci wannan matsayi ya koma gare shi ba, amma bai son annabi Adam (AS) ya ci gaba da kasancewa a ciki ba. Wannan ita ce hassada mafi muni.

2. Hassadar Yahudawa ga Musulumi:
A cikin suratul-Baƙara, Allah Ya bayyana cewa Yahudawa sun yi hassada ga Musulumi saboda Allah Ya ba su addinin da ya fi na su. Sun san gaskiya, amma sai suka ƙi amincewa da ita saboda hassada. Allah Ta’ala Ya ce:” Da yawa daga ma’abota littafi sun yi burin jna ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su.” Suratul-Baƙara aya ta 109.

Ba don Yahudawa suna son addinin Musulunci ya kasance nasu ba, sai dai kawai suna jin haushin Musulumai sun samu wannan ni’ima.

3. Hassadar ‘Yan’uwan Annabi Yusuf (AS):
‘Yan’uwan Annabi Yusuf sun yi hassada a kansa ba don suna son su zama Annabawa ba, sai dai kawai sun ƙi ganin mahaifinsu yana ƙaunarsa fiye da su. Saboda haka, suka nemi hanyar raba shi da wannan ni’ima. Allah Yana cewa:” Ka tuna lokacin da ‘yan’uwan suka ce:” Lalle Yusufu da ɗan’uwansa babammu ya fi son su da mu, ga mu kuwa jama’a masu yawa. Lalle babammu yana cikin kuskure mabayyani.” Suratu Yusuf aya ta 8.

Suna ƙyamar ganin annabi Yusuf yana cikin soyayyar mahaifinsu, har suka yi ƙoƙarin halaka shi. Wannan yana nuna yadda hassada take kai mutum ga zalunci da cutar da wasu.

4. Illolin Wannan Hassara:
Rashin Yarda da Ƙaddarar Allah: Wannan nau’in hassada yana nuna cewa mutum bai yarda da yadda Allah Yake rabon ni’ima ba. Mai irin wannan hali yana ƙin hikimar Allah da yadda Ya tsara rayuwa.

Rashin Farin Ciki da Kwanciyar Hankali: Mutum mai irin wannan hassada yana cikin damuwa a koyaushe. Yana ƙunci idan ya ga wani cikin alheri, yana fushi idan wani ya sami nasara, kuma yana jin baƙin ciki idan wani yana da wadata.

Yana Haifar da Gaba da Ƙiyayya a Tsakanin Mutane: Hassada tana haddasa gaba da ƙiyayya a tsakanin mutane. Mai irin wannan hali baya son ci gaban wasu, wanda hakan ke haifar da matsaloli a cikin al’umma.
Rashin Albarka a Rayuwa: Mutumin da yake da irin wannan hassadar ba ya samun albarka a rayuwarsa, domin Allah ba Ya albarkantar da zuciya mai kyashi da mugunta.

Allah Ya yi mana katangar ƙarfe da hasaada. Amin.

Daga
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’

Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa'

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.