• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 – AFEX

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Farashin Shinkafa Zai Ƙaru Da Kashi 40%, Masara Da Kashi 25% A Shekarar 2024 – AFEX
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton AFEX, ya ce, ya yi hasashen samun hauhawar farashin masara da shinkafa a shekarar da muke ciki ta 2024.

Rahoton wanda aka fitar ranar Laraba a Legas, ya yi hasashen samun hauhawar farashin masara da kashi 25% da kuma karin kashi 40 cikin 100 na farashin shinkafa.

A shekarar 2023, an samu sauyi mai yawa a farashin masara, inda ya kai N550,000 a cikin farko-farkon shekara, sai farashin ya rufe shekarar da kan farashin kudi N480,000. Rahoton ya danganta karuwar da raguwar kayan kan tasirin rikicin Rasha da Ukraine a farashin taki.

A bangare guda ana hasashen farashin makamashi zai ragu da kashi 5 cikin 100 a shekarar 2024 sannan ya kara raguwa da kashi 0.7 a shekarar 2025. Ana sa ran kayayyakin noma za su samu raguwar kashi 2 cikin 100 a shekarar 2024 da raguwar kashi 3 a shekarar 2025, wanda ake alakanta hakan kan rikicin Gabas ta Tsakiya.

Oluwafunto Olasemo, Mataimakin Shugaban Kasuwannin Kudi a AFEX, ya jaddada mahimmancin hangen nesa wajen daidaita hanyoyin kasuwanci da motsi a tsakanin ‘yan wasan kasuwa na zahiri da na sakandare.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Ya lura da rikitattun abubuwan daidaita yanayin siyasa, tattalin arziki, da muhalli a cikin kasuwar kayayyaki.

Olasemo ya jaddada bukatar bunkasa noma a cikin gida, daidaita kasuwanci da samar da tsare-tsare don dakile wannan matsalar da tabbatar da samar da wadataccen abinci.

Rahoton ya kuma ba da shawarar a amince da tsarin noma mai ɗorewa kamar jujjuyawar amfanin gona don inganta ƙarfin ƙasa da haɓaka yawan aiki, wanda zai iya ƙara samar da kuɗin noma da kashi 21%.

A shekarar da ta gabata alakanta samuwar irin wadannan matsaloli da kan girgizar kasa da karancin makamashi da tashe-tashen hankula da suke da jibi da siyasa da karancin kudi. Duk da waɗannan ƙalubalen, kasuwar kayayyaki ta duniya ta ragu da 24% a cikin 2022.

Kasuwanni a Nijeriya sun fuskanci koma baya sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da sauye-sauyen tattalin arziki, wanda ya haifar da karuwar kashi 0.63% a kashi uku na farkon shekarar 2023.

An samun hauhawar farashin kayayyakin noma a Nijeriya a farko saboda karancin wadata da kuma karuwar bukatar kasashen duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Farashin abinciFarashin makamashiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Aikin Hukumar Da Tinubu Ya Bai Wa Ali Nuhu Shugabanci?

Next Post

Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

3 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

15 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

16 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar

Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.