• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
AI

An rufe taron mutum-mutumin inji na duniya na 2025 yau 12 ga watan Agusta a birnin Beijing na Sin. Mahalarta daga ciki da wajen kasar Sin, ciki har da ‘yan Afirka, sun ga saurin ci gaban masana’antar fasahohin AI ta Sin da kuma sabbin abubuwan kirkire-kirkire.

 

A halin yanzu, bukatar bunkasa fasahohin AI a kasashen Afirka na karuwa cikin sauri, yayin da karfin fasahar AI na Sin ke kara ingantuwa, wanda ke baiwa sauran kasashe masu tasowa, musamman kasashen Afirka damar samun bunkasuwa bisa karfin AI. Alkaluman da aka bayar na nuna cewa, Afirka ta zama yanki na biyu mafi saurin karuwar amfani da AI a duniya. Dandalin kididdiga na Afirka ya nuna cewa a shekarar 2023, manhajoji 141 na wayar hannu masu alaka da fasahar AI sun bullo a kasuwar Afirka, wanda ya karu da kashi 24 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. Kana matsakaicin adadin masu amfani da manhajojin AI a kowane wata ya zarce miliyan 40. Manufar tattalin arzikin dijital ta Najeriya daga shekarar 2020 zuwa 2030 ta nuna cewa za a kafa cibiyar AI da mutum-mutumin inji ta kasa a nan gaba.

 

A cikin ‘yan shekarun nan, Sin da Afirka sun samar da ingantacciyar hadin gwiwa a fannin AI ta hanyar wasu tsare-tsare na kasashe biyu da na kasashe da dama, wanda ya zama muhimmin abu mafi jawo hankulan mutane a cikin hadin gwiwar Sin da Afirka. Wasu kamfanoni na Sin sun taka rawar gani wajen bunkasa kayayyakin more rayuwa na dijital a kasashen Afirka, suna ba da damar daidaita ayyuka, da hidimomi na zuba jari a fannin AI, abin da ya sa dimbin ‘yan Afirka cin gajiyarsu. A yanzu, Sin ba kawai ta zama daya daga cikin manyan kasashen da ke fitar da fasahar AI da kayayyaki zuwa Afirka ba, har ma ta hanyar kafa cibiyoyi, tana horar da matasan Afirka ilimin AI iri-iri.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

 

Lokacin da bukatun Afirka suka hadu da karfin Sin, muna da dalilin yin imani cewa, tare da tallafin dandalolin kamar su “dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC)” da shawarar “ziri daya da hanya daya”, hadin gwiwar AI tsakanin Sin da Afirka tabbas za ta samar da samako mai armashi nan gaba. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.