ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Nakiyar Ta Yi Ajalin Sojoji 5 A Borno

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya biyar ne suka mutu bayan da motarsu ta taka wata nakiya da ake zargin mayakan jihadi ne suka birne a kusa da kan iyakar Nijar, kamar yadda majiyoyin tsaro suka bayyana.

Rundunar ta kasance cikin sintiri na yau da kullun a kauyen Laayi da ke kusa da garin Damasak a ranar Litinin din da ta gabata lokacin da suka taka wata nakiya, kamar yadda wasu shugabannin mayakan biyu suka shaida wa AFP.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al’umma A Imo 
  • Kotun Sauraron Kararrakin Zabe Ta Fara Zama A Kebbi

Sojojin sun tayar da wasu bama-bamai da ake zargin kungiyar IS da ta kafa daular Islama ta yammacin Afirka (ISWAP) ce ta saka, in ji shugaban mayakan Babakura Kolo.

ADVERTISEMENT

Fashewar “Ta kashe duka sojojin biyar da ke cikin motar”, in ji shi.

Kolo ya ce mayakan jihadin sun kai hari kauyen ne a daren jiya, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna kauyen hudu da suka hada da shugaban karamar hukumar tare da dasa bama-baman yayin da suke barin kauyen.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Mai magana da yawun sojojin bai amsa kiran da AFP ta yi ba don jin ta bakinsa game da lamarin.

Shugaban ‘yan ta’adda na biyu, Ibrahim Liman, ya bayar da kididdigar adadin wadanda suka mutu.

ISWAP da ta balle daga kungiyar Boko Haram mai da’awar jihadi a shekarar 2016 ta zama babbar barazana a Nijeriya, inda ta kai hari kan sojoji da ke sintiri yayin da suke kashewa tare da yin garkuwa da fasinjoji a shingayen bincike.

Bangarorin biyu masu gaba da juna na masu jihadi sun gwabza fada a cikin ‘yan watannin da suka gabata yayin da sojoji suka zafafa kai hare-hare kan kungiyoyin.

An kafa sojojin ne a manyan sansanoni da aka fi sani a fadin yankin, lamarin da ya bar wasu kauyuka da yankunan karkara ba su da kariya da kuma fuskantar hare-hare.

A watan da ya gabata sojoji uku ne suka mutu sannan wasu hudu suka jikkata tare da wasu fararen hula bakwai a wani fashewar nakiya da ta tashi a kan wata motar soji a wajen garin Banki da ke kusa da kan iyaka da Kamaru.

Rikicin da aka kwashe shekaru 14 ana yi ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 40,000 tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Rikicin dai ya bazu zuwa wasu sassan kasashen Nijar da Chadi da Kamaru da ke makwabtaka da Nijeriya, lamarin da ya sa rundunar hadin gwiwar sojojin yankin ke yaki da mayakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10:  Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.