• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Nakiyar Ta Yi Ajalin Sojoji 5 A Borno

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya biyar ne suka mutu bayan da motarsu ta taka wata nakiya da ake zargin mayakan jihadi ne suka birne a kusa da kan iyakar Nijar, kamar yadda majiyoyin tsaro suka bayyana.

Rundunar ta kasance cikin sintiri na yau da kullun a kauyen Laayi da ke kusa da garin Damasak a ranar Litinin din da ta gabata lokacin da suka taka wata nakiya, kamar yadda wasu shugabannin mayakan biyu suka shaida wa AFP.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al’umma A Imo 
  • Kotun Sauraron Kararrakin Zabe Ta Fara Zama A Kebbi

Sojojin sun tayar da wasu bama-bamai da ake zargin kungiyar IS da ta kafa daular Islama ta yammacin Afirka (ISWAP) ce ta saka, in ji shugaban mayakan Babakura Kolo.

Fashewar “Ta kashe duka sojojin biyar da ke cikin motar”, in ji shi.

Kolo ya ce mayakan jihadin sun kai hari kauyen ne a daren jiya, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna kauyen hudu da suka hada da shugaban karamar hukumar tare da dasa bama-baman yayin da suke barin kauyen.

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Mai magana da yawun sojojin bai amsa kiran da AFP ta yi ba don jin ta bakinsa game da lamarin.

Shugaban ‘yan ta’adda na biyu, Ibrahim Liman, ya bayar da kididdigar adadin wadanda suka mutu.

ISWAP da ta balle daga kungiyar Boko Haram mai da’awar jihadi a shekarar 2016 ta zama babbar barazana a Nijeriya, inda ta kai hari kan sojoji da ke sintiri yayin da suke kashewa tare da yin garkuwa da fasinjoji a shingayen bincike.

Bangarorin biyu masu gaba da juna na masu jihadi sun gwabza fada a cikin ‘yan watannin da suka gabata yayin da sojoji suka zafafa kai hare-hare kan kungiyoyin.

An kafa sojojin ne a manyan sansanoni da aka fi sani a fadin yankin, lamarin da ya bar wasu kauyuka da yankunan karkara ba su da kariya da kuma fuskantar hare-hare.

A watan da ya gabata sojoji uku ne suka mutu sannan wasu hudu suka jikkata tare da wasu fararen hula bakwai a wani fashewar nakiya da ta tashi a kan wata motar soji a wajen garin Banki da ke kusa da kan iyaka da Kamaru.

Rikicin da aka kwashe shekaru 14 ana yi ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 40,000 tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Rikicin dai ya bazu zuwa wasu sassan kasashen Nijar da Chadi da Kamaru da ke makwabtaka da Nijeriya, lamarin da ya sa rundunar hadin gwiwar sojojin yankin ke yaki da mayakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya
Manyan Labarai

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10:  Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

Zaben Shugabannin Majalisa Ta 10: Ko Tarihi Zai Maimaita Kansa?

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.