ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fayemi Ya Taya Oyebanji Murnar Lashe Zaben Gwamnan Ekiti

Fayemi ya ce yana da yakinin Oyebanji zai dora daga inda ya tsaya.

by Sadiq
3 years ago
Ekiti

Gwamna Kayode Fayemi na Jihar Ekiti, ya ce zaben da aka yi a ranar Asabar da ta gabata na Mista Abiodun Oyebanji na jam’iyyar APC a matsayin wanda zai gaje shi zai tabbatar da ci gaba mai dorewa a jihar.

Gwamna Fayemi ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a Ado-Ekiti mai dauke da sa hannun Mista Yinka Oyebode, babban sakataren yada labaransa.

  • Masu Son Shiga Harkar Fim Su Riki Biyayya Da Kyau – Abba Harara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

Gwamnan ya taya Oyebanji murnar fitowarsa a matsayin wanda ya lashe zaben.

ADVERTISEMENT

Oyebanji ya lashe zaben ne da kuri’u 187,057, yayin da wanda ya zo na biyu, Mista Segun Oni na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), ya samu kuri’u 82,211, sai Otunba Olabisi Kolawole na PDP da ya samu kuri’u 67,457.

Fayemi ya bayyana nasarar Oyebanji a matsayin wanda ya cancanta.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Wannan abin alfahari ne da ya dace ga mutumin da ya sadaukar da lokacinaa, kuzarinsa, basirarsa da dukiyarsa wajen ci gaban jihar nan cikin shekaru 30 da suka gabata.

“Mutanen Ekiti sun yi magana da babbar murya. Sakamakon zaben ya nuna cewa mutanen Ekiti mutane ne masu mutunci, a koyaushe suna goyon bayan shugabannin da suka yi musu hidima cikin aminci.

“Ba ni da tantama cewa zababben gwamnan zai yi wa mutanen Ekiti hidima kuma ya samar da damammaki ga sauran matasa.

“Babban yabo ya tabbata ga mutanen Jihar Ekiti na gari saboda nuna wayewa a lokacin yakin neman zabe,” inji shi.

Fayemi ya kuma jinjina wa INEC kan sabbin tsare-tsare da suka sanya aka gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da inganci, da kuma yadda hukumomin tsaro suka tabbatar da gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP

Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP

LABARAI MASU NASABA

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.