ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
FIFA

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Fifa, Gianni Infantino ya yi barazanar kin nuna gasar kofin duniya ta mata ga wasu kasashen Turai biyar, matakin da ya kawo cece-kuce a duniya.

Infantino ya bukaci kasashen da cewar sai idan kamfanonin da za su haska gasar a talabijin sun kara kudin tayin da suka yi tun farko kuma shugaban ya ce abin da takaici kan kudin da aka yi tayin tallata wasannin a Burtaniya da Sifaniya da Italiya da Jamus da kuma Faransa.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ya kara da cewar an watsa wa ‘yan wasa da kwallon kafar mata kasa a ido, kuma manyan kasashen turai na shirin kawo koma baya a gasar wanda hakan abin takaici ne babba.

ADVERTISEMENT

Za’a buga gasar kofin duniya ta mata a Australia da New Zealand da za’a fara ranar 20 ga watan Yulin wannan shekarar ta 2023 sai dai Infantino ya ce kamfanonin Turai da za su tallata gasar sun yi tayin biyan dalar Amurka miliyan daya zuwa miliyan 10 idan ka kwatanta da Dalar Amurka miliyan 100 zuwa miliyan 200 wajen tallata gasar kofin duniya ta maza.

Ya ce wannan tayin ba adalci, idan suka dage iya abin da za su biya kenan, hakan zai hana Fifa ta bayar da izinin nuna gasar a kasashen sannan ya kara da cewar dukkan kudin da za’a samu a kallon gasar ta bana za’a zuba su a fannin bunkasa kwallon kafar mata a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Infantino ya ce Fifa ta kara kudin ladan lashe kofin har linki uku zuwa Dalar Amurka miliyan 152, idan aka kwatanta da abin da ta biya gasar a 2019 a kasar Faransa da aka buga.

Haka kuma Fifa na fatan biyan ladan cin kofin duniya na mata ya zama bai daya da yadda ake bai wa maza daga nan zuwa 2026/27 kamar yadda aka amince a taron da ta gudanar a cikin watan Maris.

Kamar yadda Fifa ta sanar kimanin mutum biliyan 1.12 ne suka kalli gasar kofin duniya ta mata a Faransa a shekarar 2019 kuma ita ce gasar da mutane da yawa suka kalli kwallon kafar mata a tarihi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
Wasanni

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al'ummarsa

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.