• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Fifa, Gianni Infantino ya yi barazanar kin nuna gasar kofin duniya ta mata ga wasu kasashen Turai biyar, matakin da ya kawo cece-kuce a duniya.

Infantino ya bukaci kasashen da cewar sai idan kamfanonin da za su haska gasar a talabijin sun kara kudin tayin da suka yi tun farko kuma shugaban ya ce abin da takaici kan kudin da aka yi tayin tallata wasannin a Burtaniya da Sifaniya da Italiya da Jamus da kuma Faransa.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Al’ummar Afirka Ne Ke Da Ikon Tsokaci Kan Hadin-Gwiwar Su Da Kasar Sin

Ya kara da cewar an watsa wa ‘yan wasa da kwallon kafar mata kasa a ido, kuma manyan kasashen turai na shirin kawo koma baya a gasar wanda hakan abin takaici ne babba.

Za’a buga gasar kofin duniya ta mata a Australia da New Zealand da za’a fara ranar 20 ga watan Yulin wannan shekarar ta 2023 sai dai Infantino ya ce kamfanonin Turai da za su tallata gasar sun yi tayin biyan dalar Amurka miliyan daya zuwa miliyan 10 idan ka kwatanta da Dalar Amurka miliyan 100 zuwa miliyan 200 wajen tallata gasar kofin duniya ta maza.

Ya ce wannan tayin ba adalci, idan suka dage iya abin da za su biya kenan, hakan zai hana Fifa ta bayar da izinin nuna gasar a kasashen sannan ya kara da cewar dukkan kudin da za’a samu a kallon gasar ta bana za’a zuba su a fannin bunkasa kwallon kafar mata a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

Infantino ya ce Fifa ta kara kudin ladan lashe kofin har linki uku zuwa Dalar Amurka miliyan 152, idan aka kwatanta da abin da ta biya gasar a 2019 a kasar Faransa da aka buga.

Haka kuma Fifa na fatan biyan ladan cin kofin duniya na mata ya zama bai daya da yadda ake bai wa maza daga nan zuwa 2026/27 kamar yadda aka amince a taron da ta gudanar a cikin watan Maris.

Kamar yadda Fifa ta sanar kimanin mutum biliyan 1.12 ne suka kalli gasar kofin duniya ta mata a Faransa a shekarar 2019 kuma ita ce gasar da mutane da yawa suka kalli kwallon kafar mata a tarihi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Yi Wa Aso Rock Kwaskwarima Gabanin Rantsar Da Tinubu

Next Post

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

Related

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

1 day ago
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa
Wasanni

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

2 days ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

3 days ago
Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica
Wasanni

Unity Cup: Yau Nijeriya Za Ta Buga Wasan Ƙarshe Da Ƙasar Jamaica

3 days ago
Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
Wasanni

Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa

3 days ago
Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
Wasanni

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

5 days ago
Next Post
Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al'ummarsa

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.