Filato ta tsakiya ta amince da tazarcen Gwamna Caleb Mutfwang a wa’adi na biyu a zaben shekarar 2027.
Amincewar ta biyo bayan abin da masu ruwa da tsaki suka bayyana a matsayin shugabancinsa na kishin jama’a da kawo sauyi, wanda ya yi tasiri sosai a birane da kauyuka a fadin jihar.
- Mutane 10 Sun Rasu, 29 Sun Ɓace A Mummunan Hatsarin Jirgin Ruwa A Sokoto
- Yadda Arsenal Ta Doke Manchester United Da Ci 1-0
An cimma matsayar ne a yayin wani gagarumin taron masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabannin jam’iyyar, shugabanni da jiga-jigan siyasa na shiyyar, wanda aka gudanar a Retnan Suites, Jos.
Shugaban jam’iyyar PDP na shiyyar ta tsakiya Hon. Monday Daspan, wanda ya shirya taron, ya ce Gwamna Mutfwang ya daga darajar mulki a Jihar Filato ta hanyar shugabanci na musamman da ya sa ‘yan jihar ke matukar kaunarsa.
Ya yi nuni da cewa, a cikin shekaru biyu kacal, gwamnan ya dauki kwakkwaran matakai na ci gaba, wadanda suka mayar da jihar kan turbar ci gaba mai dorewa. Ya bayyana gwamnan a matsayin “Kyautawar Allah ga Filato, wanda aka aiko domin ya farfado da sake gina jihar bisa hangen nesa na iyayen da suka kafa ta.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp