• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamfara

Matsananciyar gabar da ke tsakanin wasu kungiyoyin ‘yan bindiga da ke a Jihar Zamfara ya kara kamari inda wasu kungiyoyi hudu da suka yukura domin aiwatar da ramuwar gayya.

Wasu majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zagazola Makama cewa, wasu daga cikin kungiyoyin kuma sun yi watsi da yiwuwar kulla yarjejeniyar zaman lafiya a kan sauran, yayin da suke shelanta ci gaba da yin adawa da sauran.

  • Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi
  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2

A ranar Asabar din da ta gabata, 14 ga Afrilu, 2024, wakilan kungiyoyin uku daga cikin hudu – Dan Karami Gwaska da Alhaji Shingi, sun yi taro a Kauyen Usu da ke Karamar Hukumar Birnin-Magaji domin tattaunawa a tsakaninsu. Kungiyar Bello Turji ba ta halarci taron ba.

Ado Aleru ya wakilci kungiyar Alhaji Shingi; Bello Tagoje ya wakilci kungiyar Kachalla Halilu; yayin da Ardo Na-shawari, Alhaji Ali, Alhaji Shamago da dan Karami Gwaska suka wakilci kungiyar Gwaska.

Kungiyar ta Shingi wanda Ado Aleru ya wakilta, ta yi gargadi ga kungiyar Gwaska cewa kada ta sake sanya kafarta a al’ummar Tsanu da Rukudawa na Karamar Hukumar Zurmi. Sun kuma yi gargadin cewa idan Gwaska ya yi watsi da gargadin da suka yi masa, za su kashe shi da wasu daga cikin mutanensa.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

A ci gaba da fafatawa da su shugabannin ‘yan bindiga uku, Ado Allero, Dan Yusufa da Mali sun riga sun ajiye mutanensu a Arewacin Tsafe, a shirye-shiryen tunkarar duk wata arangama.

A matsayin wani sharadi na zaman lafiya kuwa, kungiyar ta Shingi ta bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa wani Hassan shanun da ya sace a Bafashi na Karamar Hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Sun kuma bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa Sani Dangote makaman da ya kwace masa a makon da ya gabata; sannan kuma ya sayi sabbin babura a matsayin diyya ga wadanda ya kona na mutanen Dangote.

Kungiyar Dan Karami Gwaska ta amince da dukkan sharuda.

Sai dai Bello Turji, wanda bai halarci taron ba, ballantana ya tura wakilai, ya yi watsi da yiwuwar samun zaman lafiya tsakaninsa da Gwaska, inda ya tabbatar da cewa zai ci gaba da farautar Gwaska har ya ga bayansa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Next Post
Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci – Bankin Duniya

Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa 'Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci - Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.