• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsananciyar gabar da ke tsakanin wasu kungiyoyin ‘yan bindiga da ke a Jihar Zamfara ya kara kamari inda wasu kungiyoyi hudu da suka yukura domin aiwatar da ramuwar gayya.

Wasu majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zagazola Makama cewa, wasu daga cikin kungiyoyin kuma sun yi watsi da yiwuwar kulla yarjejeniyar zaman lafiya a kan sauran, yayin da suke shelanta ci gaba da yin adawa da sauran.

  • Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi
  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2

A ranar Asabar din da ta gabata, 14 ga Afrilu, 2024, wakilan kungiyoyin uku daga cikin hudu – Dan Karami Gwaska da Alhaji Shingi, sun yi taro a Kauyen Usu da ke Karamar Hukumar Birnin-Magaji domin tattaunawa a tsakaninsu. Kungiyar Bello Turji ba ta halarci taron ba.

Ado Aleru ya wakilci kungiyar Alhaji Shingi; Bello Tagoje ya wakilci kungiyar Kachalla Halilu; yayin da Ardo Na-shawari, Alhaji Ali, Alhaji Shamago da dan Karami Gwaska suka wakilci kungiyar Gwaska.

Kungiyar ta Shingi wanda Ado Aleru ya wakilta, ta yi gargadi ga kungiyar Gwaska cewa kada ta sake sanya kafarta a al’ummar Tsanu da Rukudawa na Karamar Hukumar Zurmi. Sun kuma yi gargadin cewa idan Gwaska ya yi watsi da gargadin da suka yi masa, za su kashe shi da wasu daga cikin mutanensa.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

A ci gaba da fafatawa da su shugabannin ‘yan bindiga uku, Ado Allero, Dan Yusufa da Mali sun riga sun ajiye mutanensu a Arewacin Tsafe, a shirye-shiryen tunkarar duk wata arangama.

A matsayin wani sharadi na zaman lafiya kuwa, kungiyar ta Shingi ta bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa wani Hassan shanun da ya sace a Bafashi na Karamar Hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Sun kuma bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa Sani Dangote makaman da ya kwace masa a makon da ya gabata; sannan kuma ya sayi sabbin babura a matsayin diyya ga wadanda ya kona na mutanen Dangote.

Kungiyar Dan Karami Gwaska ta amince da dukkan sharuda.

Sai dai Bello Turji, wanda bai halarci taron ba, ballantana ya tura wakilai, ya yi watsi da yiwuwar samun zaman lafiya tsakaninsa da Gwaska, inda ya tabbatar da cewa zai ci gaba da farautar Gwaska har ya ga bayansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Taba Iya Aure Ko Zama Da Wanda Ba Ya Son Sana’ar Dana Ke Yi Ba -Asmee Wakili

Next Post

Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci – Bankin Duniya

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

3 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

4 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

6 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

7 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

8 hours ago
Next Post
Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci – Bankin Duniya

Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa 'Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci - Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.