ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
NDLEA

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi Ta Kasa NDLEA sun damke wata motar haya bas dauke da jabun kudi Naira miliyan 3.2 mallakar wasu mutum uku: Fabour Peter mai ciki wata takwas mai shekaru 24; Esther Adukwu, mai shekaru 27 da Ochigbo Michael, mai shekaru 39, wadanda aka kama a tashar mota ta Jabi da ke Abuja, a wani sumame da aka kai ranar Talata, 9 ga watan Afrilu, 2024, biyo bayan kama wasu kudaden na jabun Naira a Lokoja, jihar Kogi.

Hakan ta faru ne a daidai lokacin da jami’an NDLEA tare da hadin gwiwar rundunar sojojin ruwan Nijeriya da ke Lugard Base a Lokoja suka kama wani Aliyu Lawal dan shekara 37 a hanyar Lokoja zuwa Abuja ranar Litinin, tare da kwato dauri 620 na tabar wiwi mai nauyin kilogiram 310 daga gare shi, yayin da jami’an NDLEA ta kama Jama Obodo, mai shekaru 44, da buhu 10 na wannan taba mai nauyin kilogiram 98 a kan titin Okene zuwa Lokoja-Abuja a cikin wata motar haya bas da ta taso daga Ilesha, jihar Osun ta hanyar zuwa Jihar Taraba a Afrilu.

  • Wata Kungiya Ta Shirya Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi 400,000 A Nijeriya
  • Jihar Benuwai Ta Bankado Mutum 35 Masu Yi Wa Sirin Tattara Harajinta Zagon-Kasa

A Jihar Kuros Riba, an kama wata bazawara mai shekaru 40 da haihuwa kuma mahaifiyar ‘ya’ya biyu, Misis Theodora a Bassey Edom, Calabar, sannan jami’an sun kama wata mata mai shekaru 40 da haihuwa a garin Bassey Edom da ke Calabar bisa laifin hadawa gami da sayar da wani sabon sinadari mai saurin kisa, NPS, a cikin gida. mai suna ‘Combine’, wato a hda gami da cakuda nau’ikan cannabis daban-daban da opioids wadanda aka jika a cikin danyen sinadarin Gin.

ADVERTISEMENT

A lokacin da aka kama ta, an kwato lita 18 na sinadari mai hatsarin gaske a cikin bokitin  fenti.

Yayin dake amsa tambayoyi, ta yi ikirarin cewa ta fara samar da wadannan haramtattun magunguna ne da rarrabawa a watan Oktoban 2023. Wani wanda ake zargi, Godwin Okon Samuel, mai shekaru 48, an kama shi a unguwar Essit Ebum da ke Calabar da kilogiram 39.4 na tabar wiwi a ranar Talata, 9 ga Afrilu.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Yayin da aka kama wasu mutum biyu: Sani Mohammed, mai shekaru 43, da Christopher Eze, mai shekaru 64 a unguwar Sabon Gari dake Kano a ranar Talata, 9 ga watan Afrilu, tare da kwato kwayoyi na opioid 900,000 daga hannunsu, jami’an NDLEA da ke sintiri a hanyar Owerri-Onitsha, Jihar Imo, a ranar Juma’a, 12 ga Afrilu, ta kama wata babbar motar daukar kaya mai lamba JGB 403DB, inda ta gano cannabis 230 na Satiba mai nauyin kilogiram 119 da aka boye a karkashin kayayyakin gida, bayan tsananta bincike.

 An kama akalla kilogiram 252 na tabar wiwi yayin wani samame da aka kai dajin Ijesa Isu, Jihar Ekiti a ranar Asabar 13 ga watan Afrilu yayin da wasu mutum hudu: Adamu Umar, mai shekaru 39; Abdullahi A Gimba, mai shekaru 27; da kuma Julius Uduakhomu, mai shekaru 28; an kama Micheal Sunday, mai shekaru 24, suna lodin kilogiram 40 na kaya maye a dakin da aka ajiye injin wata motar gas a kauyen Agho dake yankin Owan ta Gabas ta Jihar Edo.

An kuma gano babura biyu da aka yi amfani da su wajen kai kayan zuwa inda motar iskar gas din ta nufa.

A Jihar Ogun, an kama wani da ake zargi mai suna Ismaila Ogun a ranar Juma’a, 12 ga watan Afrilu da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 79 a Imeko, yayin da aka kama wani matashi mai suna Friday Abah mai shekaru 18 da kilogiram 410 na irin wannan taba a lokacin da jami’an NDLEA suka kai farmaki sansanin Obatedo, dajin Itaogbolu, a Karamar Hukumar Akure ta Arewa, Jihar Ondo.

 Wata sanarwa da Daraktan Yada labarai da bayar da shawarwari Femi Babafemi,ya fitar a shalkwatar hukumar ta NDLEA da ke Abuja, ya ce da irin wannan himma, tare da ba da umarni daban-daban na hukumar a fadin kasar nan, jami’an sun ci gaba da fafutukar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Wasu daga cikin ayukan sun hada da: Lakcar wayar da kan dalibai da ma’aikatan Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gboko, a Gboko, Jihar Binuwai, wato WADA; Hafsoshin soji da mutum 15 na ‘Engineering Field Regiment Nigerian Army’, Topo, Badagry Lagos; mahautar nama ta Odo Eran, Osogbo, Jihar Osun kai ziyarar gami da ba da shawarwari ga Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, da dai sauransu.

Yayin da yake yaba wa Hafsoshi da jami’an Kogi, Cross Riber, Ondo, Ekiti, Ogun, Imo, Kano, da Edo na hukumar kwamandojin hukumar bisa bajintar da suka yi wajen rage yawan shan miyagun kwayoyi, Babban Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya), ya kuma yaba musu da takwarorinsu na dukkan bangarorin kasar nan kan yadda suka karfafa lakcocinsu na ‘WADA’, da nufin rage sha’awar shan miyagun kwayoyi.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.