ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Zamfara

Matsananciyar gabar da ke tsakanin wasu kungiyoyin ‘yan bindiga da ke a Jihar Zamfara ya kara kamari inda wasu kungiyoyi hudu da suka yukura domin aiwatar da ramuwar gayya.

Wasu majiyoyin leken asiri sun shaida wa Zagazola Makama cewa, wasu daga cikin kungiyoyin kuma sun yi watsi da yiwuwar kulla yarjejeniyar zaman lafiya a kan sauran, yayin da suke shelanta ci gaba da yin adawa da sauran.

  • Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi
  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2

A ranar Asabar din da ta gabata, 14 ga Afrilu, 2024, wakilan kungiyoyin uku daga cikin hudu – Dan Karami Gwaska da Alhaji Shingi, sun yi taro a Kauyen Usu da ke Karamar Hukumar Birnin-Magaji domin tattaunawa a tsakaninsu. Kungiyar Bello Turji ba ta halarci taron ba.

ADVERTISEMENT

Ado Aleru ya wakilci kungiyar Alhaji Shingi; Bello Tagoje ya wakilci kungiyar Kachalla Halilu; yayin da Ardo Na-shawari, Alhaji Ali, Alhaji Shamago da dan Karami Gwaska suka wakilci kungiyar Gwaska.

Kungiyar ta Shingi wanda Ado Aleru ya wakilta, ta yi gargadi ga kungiyar Gwaska cewa kada ta sake sanya kafarta a al’ummar Tsanu da Rukudawa na Karamar Hukumar Zurmi. Sun kuma yi gargadin cewa idan Gwaska ya yi watsi da gargadin da suka yi masa, za su kashe shi da wasu daga cikin mutanensa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

A ci gaba da fafatawa da su shugabannin ‘yan bindiga uku, Ado Allero, Dan Yusufa da Mali sun riga sun ajiye mutanensu a Arewacin Tsafe, a shirye-shiryen tunkarar duk wata arangama.

A matsayin wani sharadi na zaman lafiya kuwa, kungiyar ta Shingi ta bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa wani Hassan shanun da ya sace a Bafashi na Karamar Hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Sun kuma bukaci Dan Karami Gwaska ya mayar wa Sani Dangote makaman da ya kwace masa a makon da ya gabata; sannan kuma ya sayi sabbin babura a matsayin diyya ga wadanda ya kona na mutanen Dangote.

Kungiyar Dan Karami Gwaska ta amince da dukkan sharuda.

Sai dai Bello Turji, wanda bai halarci taron ba, ballantana ya tura wakilai, ya yi watsi da yiwuwar samun zaman lafiya tsakaninsa da Gwaska, inda ya tabbatar da cewa zai ci gaba da farautar Gwaska har ya ga bayansa.

Zamfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci – Bankin Duniya

Hauhawar Farashi Ta Sake Jefa 'Yan Nijeriya Miliyan 10 Cikin Talauci - Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.