Hon. Sanusi Ibrahim Yaro, Darakta Janar na Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu na kasa (STSG), ya bayyana cewa; nan ba jimawa ba, za su yi gangamin taronsu na kasa baki-daya.
“Za mu yi wannan gangamin taro ne, domin sake tabbatar da samun nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a karo na biyu, wanda muke sa ran aiwatar da taron nan da ‘yan wasu makwanni kadan masu zuwa,” in ji Yaro.
- ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum
- Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha
Ibrahim ya ci gaba da cewa, suna nan suna ci gaba da aiki babu dare babu rana, domin kuwa maganar da ake yi yanzu, dukkanin jihohin Arewacin wannan kasa da wasu daga cikin jihohin kudancin ƙasar nan, na nan suna shirya tarukansu daban-daban, kafin wannan babban taro da za a aiwatar na kasa a babban birnin tarayya Abuja.
“Tunda aka kafa wannan kungiya, ba mu yi kasa a gwiwa ba wajen tallata ayyuka da manufofin wannan gwamnati ga musamman ‘yan’uwanmu matasa maza da mata, don sanin irin kokarin da shugaban kasa ke yi na ciyar da wannan kasa gaba.”
Har ila yau, a cewar Hon. Yaro; sun yi wa wannan ƙungiya lakabi da sunan Seyi Tinubu (STSG) ne, saboda jajircewar Seyi Tinubun a kan matasa maza da mata.
Kazalika ya kara da cewa, idan za a iya tunawa, Seyi ya kewaya kusan dukkanin jihohin Arewacin kasa nan tare da tallafa wa al’umma da kayan abinci da kudade, musamman a watan Ramadana da ya gabata.
A karshe, Sanusi ya yi kira ga matasa maza da mata, kada su bari a bar su a baya a wannan tafiya, domin kuwa kungiya ta kowa da kowa ce, duk mai bukatar yin rajista; kofa a bude take, domin kuwa suna da ofisoshi a kowace jiha, ciki har da babban birnin tarayya Abuja da suke shirin bude kwanan nan ga masu bukatar shiga.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp