• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inuwar gamayyar masu ruwa da tsaki a kan ilimi a Jihar Kano sun nuna goyon bayansu na kwato muhallan makarantu da gwamnatin mai ci yanzu ta ke yi.

Dakta Ibrahim Usman Aikawa ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da suka gudanar a ranar Talata.

  • An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Ya ce taron nasu na wayarwa da mutane kai ne, a kan martabar da darajar ilimi da nuna goyon baya ga matakai da gwamnati a Jihar Kano ta dauka a kan filayen makarantu da ake karbowa.

Ya yi nuni da cewa suna sane da cewa wasu za su samu rashin jindadi a kan abin da yake faruwa amma wannan abu an yi shi ne don ci gaban al’umma domin magabata sun san martaba na ilimin Addinin dana boko saboda daraja da girmama ilimi Manzon Allah ya yi umarni aje a nemi ilimi ko a birnin Sin ne.

Dakta Aikawa, ya ce “marigayi Nelson Mandela na Afirka ta Kudu, ya ce ilimi ne makami da za ka yi amfani da shi da za ka iya juya duniya ta abin da kake so, amma a wannan yanayin ne aka samu wasu marasa kishi da rashin kaunar ci gaban ilimi a Kano suka handame filayen makarantu suka mayar da su gidaje da shaguna da wajen taron biki da wasanni.”

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

Ya ce duk wanda ya yi korafi a kan an rushe masa gida cewa yake a filin Salanta, ba sa cewa a filin makarantar Kano Poly saboda sanin idan suka fadi haka kowa zai gane sun shiga harkar filin ne.

Ya ce akwai wanda ya ce ya kashe miliyan 800 a gininsa duk wanda zai iya kashe irin wannan kudi ya gina gida da wuya a samu iyalansa na zuwa makarantun gwamnati sai wanda zai biya ko ba a kasar nan ba su yi karatu, amma ya zo ya debi kayan talakawa ya yi gini a kai saboda ana so a mallake ‘yancin talaka a hana ‘ya’yansu ilimi.

Aikawa, ya yi kira ga Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf a kan ya ci gaba da daukar matakai irin wadannan na rushe gini da aka yi ba bisa ka’ida ba, a kan zalunci don rusa ilimi a Jihar Kano.

Ya kara da cewa ya kamata a dauki tsauraran matakai na yin dokoki don hana wani nan gaba ya sake sayar da wajen makarantu na al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGamayyar Masu Ruwa TsakikanoRusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato

Next Post

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

4 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

5 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

6 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

7 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

7 hours ago
Next Post
EFCC Ta Tsare Tsohon Gwamnan Benuwe, Ortom

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa'o'i

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.