• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inuwar gamayyar masu ruwa da tsaki a kan ilimi a Jihar Kano sun nuna goyon bayansu na kwato muhallan makarantu da gwamnatin mai ci yanzu ta ke yi.

Dakta Ibrahim Usman Aikawa ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da suka gudanar a ranar Talata.

  • An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Ya ce taron nasu na wayarwa da mutane kai ne, a kan martabar da darajar ilimi da nuna goyon baya ga matakai da gwamnati a Jihar Kano ta dauka a kan filayen makarantu da ake karbowa.

Ya yi nuni da cewa suna sane da cewa wasu za su samu rashin jindadi a kan abin da yake faruwa amma wannan abu an yi shi ne don ci gaban al’umma domin magabata sun san martaba na ilimin Addinin dana boko saboda daraja da girmama ilimi Manzon Allah ya yi umarni aje a nemi ilimi ko a birnin Sin ne.

Dakta Aikawa, ya ce “marigayi Nelson Mandela na Afirka ta Kudu, ya ce ilimi ne makami da za ka yi amfani da shi da za ka iya juya duniya ta abin da kake so, amma a wannan yanayin ne aka samu wasu marasa kishi da rashin kaunar ci gaban ilimi a Kano suka handame filayen makarantu suka mayar da su gidaje da shaguna da wajen taron biki da wasanni.”

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Ya ce duk wanda ya yi korafi a kan an rushe masa gida cewa yake a filin Salanta, ba sa cewa a filin makarantar Kano Poly saboda sanin idan suka fadi haka kowa zai gane sun shiga harkar filin ne.

Ya ce akwai wanda ya ce ya kashe miliyan 800 a gininsa duk wanda zai iya kashe irin wannan kudi ya gina gida da wuya a samu iyalansa na zuwa makarantun gwamnati sai wanda zai biya ko ba a kasar nan ba su yi karatu, amma ya zo ya debi kayan talakawa ya yi gini a kai saboda ana so a mallake ‘yancin talaka a hana ‘ya’yansu ilimi.

Aikawa, ya yi kira ga Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf a kan ya ci gaba da daukar matakai irin wadannan na rushe gini da aka yi ba bisa ka’ida ba, a kan zalunci don rusa ilimi a Jihar Kano.

Ya kara da cewa ya kamata a dauki tsauraran matakai na yin dokoki don hana wani nan gaba ya sake sayar da wajen makarantu na al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGamayyar Masu Ruwa TsakikanoRusau
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato

Next Post

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i

Related

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

21 minutes ago
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
Labarai

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

1 hour ago
Kano
Labarai

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

2 hours ago
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu
Labarai

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

2 hours ago
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle
Labarai

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

5 hours ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

6 hours ago
Next Post
EFCC Ta Tsare Tsohon Gwamnan Benuwe, Ortom

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa'o'i

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
Kano

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

May 10, 2025
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

May 10, 2025
Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

Mambobin APC Sun Buƙaci EFCC Ta Sake Buɗe Binciken Matawalle

May 10, 2025
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

May 10, 2025
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.