• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

by Bello Hamza
2 years ago
Kano

Inuwar gamayyar masu ruwa da tsaki a kan ilimi a Jihar Kano sun nuna goyon bayansu na kwato muhallan makarantu da gwamnatin mai ci yanzu ta ke yi.

Dakta Ibrahim Usman Aikawa ne, ya bayyana haka a taron manema labarai da suka gudanar a ranar Talata.

  • An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Ya ce taron nasu na wayarwa da mutane kai ne, a kan martabar da darajar ilimi da nuna goyon baya ga matakai da gwamnati a Jihar Kano ta dauka a kan filayen makarantu da ake karbowa.

Ya yi nuni da cewa suna sane da cewa wasu za su samu rashin jindadi a kan abin da yake faruwa amma wannan abu an yi shi ne don ci gaban al’umma domin magabata sun san martaba na ilimin Addinin dana boko saboda daraja da girmama ilimi Manzon Allah ya yi umarni aje a nemi ilimi ko a birnin Sin ne.

Dakta Aikawa, ya ce “marigayi Nelson Mandela na Afirka ta Kudu, ya ce ilimi ne makami da za ka yi amfani da shi da za ka iya juya duniya ta abin da kake so, amma a wannan yanayin ne aka samu wasu marasa kishi da rashin kaunar ci gaban ilimi a Kano suka handame filayen makarantu suka mayar da su gidaje da shaguna da wajen taron biki da wasanni.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ya ce duk wanda ya yi korafi a kan an rushe masa gida cewa yake a filin Salanta, ba sa cewa a filin makarantar Kano Poly saboda sanin idan suka fadi haka kowa zai gane sun shiga harkar filin ne.

Ya ce akwai wanda ya ce ya kashe miliyan 800 a gininsa duk wanda zai iya kashe irin wannan kudi ya gina gida da wuya a samu iyalansa na zuwa makarantun gwamnati sai wanda zai biya ko ba a kasar nan ba su yi karatu, amma ya zo ya debi kayan talakawa ya yi gini a kai saboda ana so a mallake ‘yancin talaka a hana ‘ya’yansu ilimi.

Aikawa, ya yi kira ga Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf a kan ya ci gaba da daukar matakai irin wadannan na rushe gini da aka yi ba bisa ka’ida ba, a kan zalunci don rusa ilimi a Jihar Kano.

Ya kara da cewa ya kamata a dauki tsauraran matakai na yin dokoki don hana wani nan gaba ya sake sayar da wajen makarantu na al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
EFCC Ta Tsare Tsohon Gwamnan Benuwe, Ortom

EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa'o'i

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.