• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Game Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya

by Ra'ayinmu
10 months ago
in Ra'ayinmu
0
Game Da Tsadar Rayuwa A Nijeriya

Tashin farashi

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotannin na nuna cewa, wasu da ba a san ko su wanene ba suna shirin jagorantar gudanar da gaggarumar zanga-zanga shigen irin wannan da aka yi shekarun baya mai suna #EndSARS, sun shirya zanga-zangar ne don kalubalantar tsananin tsadar rayuwa da ake fuskanta a Nijeriya. Wadanda suka bayar da wa’adin fara zanga-zangar suna ganin cewa, gwamnatin tarayya ba ta yi abin da ya kamata ba domin maganin matsalar tsadar abinci da ake fuskanta wanda yake neman jefa al’umma cikin halin ni ‘ya su. Mun dauki wannan lamarin da muhimmanci sosai, ya kuma kamata a gaggauta daukar matakin ganin an kawo karshensa.

Masana na da ra’ayin cewa, rikicin ya taso ne sanadiyyar matsalar tsadar abinci tana iya barazana ga tsaron kasa gaba daya. Ba bama-baman nukiliya suka rusa daular gurguzu ta rasha ba.  Matsalar tsadar rayuwa ce haifar da juyin juya hali na kasar Faransa. Kuma gashi kasar nan ta yi shekara 15 tana fuskantar yaki da ta’addanci da harkokin ‘yan bindiga. Kara matsalar tsadar abinci a ra’ayinmu, wani abu ne da ba zai haifar wa Nijeriya da da mai ido ba. Matsalar tattalin arzikin da ake ciki ta jefa ‘yan Nijeriya da dama cikin wahalar samun cin abincin yau da kullum a cikin sauki. Harkokin rayuwa suna kara hauhawa a kullum, farashin kayan masarufi, man fetur da wutar lantarki sun yi tashin gwauron zabo, a kullum kuma abin kara tashi suke yi.

  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Majalisa Sun Rage Albashinsu Da Kashi 50 Cikin 100
  • Zanga-zanga: Minista Ya Nemi Jama’a Su Ƙara Haƙuri, Gwamnati Na Ƙoƙarin Rage Tsadar Rayuwa 

A hasashen ta na baya-bayan nan, Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya fiye da Miliyan 82 kusan kashi 64 na al’ummar kasar za su fuskanci yunwa nan da shekarar 2030. A kan haka ne majalisar ta nemi gwamnati ta dauki matakan dakile dumamar yanayi, barazanar kwari da sauran matsalolin da ke dakile harkar noma a kasar nan. A halin yanzu saura shekara 6 a kai shekarar 2030 amma lallai ya kamata mahukunta su natsu su yi tunani tare da fitar da hanyoyin da za a kauce wa fadawa matsalar yunwa da rashin abinci a kasar nan.

A matsayinmu na gidan jarida, muna kara tunatar da gwamnati nauyin da ke a kanta wanda ya hada da samar da jin dadin rayuwa ga al’umma, wanda hakki ne da tsarin mulkin kasa ya dorawa gwamnati na ta tabbatar da jin dadi da tsaron al’umma ba tare da nuna banbanci ba.

Duk da haka muna kira ga gwamnati da ta yi mai yiwuwa na hana wa duk wata kungiyar hujjar shiga wata zanga-zanga, abin da zai iya jefa kasar matsalar da ya yi kamata da ta #EndSARS. Wanda aka yi shekarun baya mun ga yadda aka yi asarar rayukan mutane aka kuma barnatar da dukiyoyin al’umma. Zuwa yanzu kasar bata farfado daga abin da ya faru a wancan lokacin ba, saboda haka bai kamata a kara jefa amu cikin wata zanga-zangar da zai iya zama mafi muni fiye da na baya ba.

Labarai Masu Nasaba

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

Kwanakin baya, Majalisar Dattawa ta nemi gwamnatin tarayya ta gaggauta maganin tsadar rayuwa da mastalar abinci da ake fuskanta, ta kuma nemi ta yi wani abu a kan karin kudin wutar lantarki da aka yi don kada a jefa kasar cikin rudanin da zai iya haifar da mastalolin da ba za mu iya dauka ba. Majalisar Dattawa ta sa baki ne ganin abin da ke faruwa a kasar Kenya kwanan nan, inda aka yi wa gwamnati bore saboda karin kudin haraji, inda matasa ke neman a inganta rayuwar al’ummar kasar, sun kuma nemi Shugaban Kasa William Ruto ya yi murabus.

A mastayinmu na gidan jarida, hakki ne a kanmu musamman ganin mune keda hakkin sa ido a kan al’ummuran gwamnati da yadda suke shafar al’umma, mu yi magana domin duk abin da zai faru ya shafe mu a mastayinmu na ‘yan Nijeriya. Muna masu yaba wa gwamnati a kan tallafin tirela 20 da ta bai wa kowace jiha wanda aka shirya raba wa ‘yan Nijeriya fiye da miliyan 163 da ke fuskanta matsalar rashin abinci. Amma wannan tallafin ba zai kai ko ina ba in aka lura da yawan al’ummar da ke fuskantar matsalar rashin abinci.

Kari ga wadancan tileloli na abin da aka tura wa jihohi, ya kamata gwamnatin tarayya ta gaggauta daukar matakin dawo da tallafin da ta janye a wutar lantarki, man fetur da kuma matsalar rashin daidato na farashin Naira a kasuwannin kasashen waje wanda yake cutar da manya da kananan kamfanoni da kuma al’ummar Nijeriya da ke a kan titunan kasar nan.

A kan haka yana da matukar muhimmanci gwamnati a dukkan matakai su dauki matakai masu muhimmanci na kawo karshen matsalar tsadar raywua da al’umma ke fuskanta. Wannan ba lokaci ne na alkawaurran da ba za a iya cikawa ba, mutane na bukatar a dauki matakin da za su iya gani a kasa ne ba tare da bata lokaci ba.

A kan zanga-zangar tsadar rayuwa da ake shiryawa a fadin Nijeriya, muna kira ga gwamnati da ta dauki matakin yayyafawa shirin ruwa, kada kuma a dauki matakin musgunawa ga matasan da za su fito kan titi domin kuwa lallai al’umma na fama da yunwa, kuma hakki ne na gwamnati ta samar wa al’umma abinci. Lokaci ya yi da gwamnati za ta dauki mataki na kawo karshen matsalolin da al’umma ke fuskanta. Dole gwamnati ta dauki darasi daga gargadin ‘William Shakespeare’ inda ya ce, “Ka yi hankali fushin mai jin yunwa”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FoodsInflationTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Gasar Olympics Alama Ce Ta Hadin Gwiwa Da Zumunci Da Ci Gaban Da Aka Samu Ta Fuskar Koyi Da Juna a Bangaren Al’adu

Next Post

Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa

Related

Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

2 weeks ago
NCC
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

2 months ago
Ra'ayinmu

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

3 months ago
Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya
Ra'ayinmu

Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya

4 months ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Ra'ayinmu

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

5 months ago
Matasa 5 Cikin Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Sun yanke Jiki Sun Faɗi A Kotu
Ra'ayinmu

Batun Tuhumar Ƙananan Yara Da Laifin Shirya Juyin Mulki

6 months ago
Next Post
Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa

Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.