• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu kallo ya koma sabon babin da aka bude na kyautata alaka a tsakanin giwayen kasashen duniya biyu, Sin da Amurka yayin da aka yi ganawar keke-da-keke a tsakanin Shugaba Xi Jinping da takwaransa Joe Biden a birnin San Francisco na Amurka, ranar Laraba.

Bayan ganawar, shugabannin biyu sun jaddada muhimmancin dake akwai na dukkan kasashen duniya su mutunta juna da kuma samar da hanyar zama cikin lumana da barin kofofin sadarwa a bude tare da dakile rikici.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC
  • Wakilan Sin Da Kenya Sun Halarci Dandalin Tattaunawa Kan Hanyoyin Zamanintar Da Kasa

Sun amince da karfafa tattaunawa da hadin gwiwa a bangarori daban-daban, ciki har da kafa wata gamayya da za ta yi aiki kan yaki da muggan kwayoyi, da maido da manyan hanyoyin sadarwa na soja da kuma tinkarar matsalar sauyin yanayi tare.

Kamar yadda shugaban cibiyar bincike kan al’amuran kasar Sin ta 22V Research, Michael Hirson ya fada, ganawar shugabannin biyu za ta zama rigakafin magance rikicin da babu wanda yake da muradin gani a tsakaninsu.

Sabanin Amurka da Sin ya karu a shekarun baya musamman a karkashin gwamnatin Trump sakamakon kare-karen haraji da kuma takunkuman fasaha a karkashin gwamnatin Biden.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Sai dai alaka ta fara kyautatuwa bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kai wata ziyara a birnin Beijing a watan Yuni, kana a farkon watan Oktoba, shugaban masu rinjaye na majalisar dattijan Amurka Chuck Schumer da wasu ’yan majalisar dattawan Amurka biyar dake wakiltar jam’iyyun Republican da Democrat, sun yi wata ganawa ta mintuna 80 da shugaba Xi Jinping.

“Dangantakar da ake gani a halin yanzu tsakanin Sin da Amurka ta sa duniya ta numfasa”, a cewar Shen Yamei, daraktan sashen nazarin Amurka, kuma abokiyar bincike a cibiyar nazarin kasa da kasa ta kasar Sin.

Kamar yadda Shugaba Xi ya sha nanatawa a baya kuma ya sake jaddada a yanzu, gasa mara tsafta a tsakanin manyan kasashen duniya ba ita ake yayi ba a wannan zamanin, a cewarsa, duniya tana da fadin da manyan kasashen biyu za su sakata su wahala cikin nasara. Don haka samun nasarar kowace kasa a tsakaninsu, wata dama ce ta ci gaba ga ’yar ’uwarta.

Abin sha’awa da kuma ke nuna shugabannin biyu sun hau turba guda, shi ma shugaba Biden ya sha alwashin cewa ba zai mayar da gasa a tsakanin kasashen biyu ta zama ta rikici ba, ya kuma yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa don tunkarar kalubalen duniya.

Wani abu dake kara nuna cewa Sinawa da Amurkawa na da kyakkyawar fatan cin moriyar juna shi ne, yadda sama da masu baje kolin Amurka 200 daga bangaren noma, na’urori masu sarrafa kwamfuta, na’urorin likitanci, motocin zamani masu aiki da sabbbin makamashi, kayan kwalliya, da dai sauransu suka halarci bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su na kasar Sin karo na shida (CIIE) da aka kammala kwanan nan a Shanghai. Ba a taba samun Amurkawa masu yawa da suka halarci bikin kamar a bana ba a tarihin bikin baje kolin.

A cewar bankin duniya, Amurka tana da karfin hada-hadar tattalin arziki na GDP na a kalla tiriliyan 25.5 a bara, yayin da na Sin ya kai kusan dala tiriliyan 17.9, wanda ya kai sama da kashi uku na tattalin arzikin duniya idan aka hade. Kasar Sin da Amurka suna da kusan kashi daya bisa hudu na al’ummar duniya, kuma cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya kai kusan kashi biyar na jimillar na duniya kaf.

Ba Amurka da Sin kawai idan dangantaka mai gwabi ta dore a tsakaninsu zai amfanar ba har da sauran kasashen duniya, kasancewar hakan za ta kara bude sabbin hanyoyin cinikayya musamman ganin cewa kasashen biyu ke da kashi daya bisa hudun yawan al’ummar duniya.

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana a jawabinsa na bude taron kasashen biyu a ranar Laraba, “akwai bukatar manyan kasashen su rika nuna cewa su manya ne a aikace” saboda hakan na da matukar muhimmanci ga samar da ci gaban duniya cikin hanzari da ba a ga irinsa ba cikin karni.

Muna fata zumunci ya dore tare da kauce wa komawa ’yar gidan jiya.( Abdulrazaq Yahuza)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenSan FranciscoXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Adalci Ne Karbe Kashi 40 Cikin 100 Na Kudaden Shigar Jami’oi (1)

Next Post

Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

1 hour ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

3 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

3 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

7 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

9 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

9 hours ago
Next Post
Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Ba Ni Da Sha'awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba - Omorodion

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.