ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

by CGTN Hausa
3 years ago
Francisco

A halin yanzu kallo ya koma sabon babin da aka bude na kyautata alaka a tsakanin giwayen kasashen duniya biyu, Sin da Amurka yayin da aka yi ganawar keke-da-keke a tsakanin Shugaba Xi Jinping da takwaransa Joe Biden a birnin San Francisco na Amurka, ranar Laraba.

Bayan ganawar, shugabannin biyu sun jaddada muhimmancin dake akwai na dukkan kasashen duniya su mutunta juna da kuma samar da hanyar zama cikin lumana da barin kofofin sadarwa a bude tare da dakile rikici.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC
  • Wakilan Sin Da Kenya Sun Halarci Dandalin Tattaunawa Kan Hanyoyin Zamanintar Da Kasa

Sun amince da karfafa tattaunawa da hadin gwiwa a bangarori daban-daban, ciki har da kafa wata gamayya da za ta yi aiki kan yaki da muggan kwayoyi, da maido da manyan hanyoyin sadarwa na soja da kuma tinkarar matsalar sauyin yanayi tare.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban cibiyar bincike kan al’amuran kasar Sin ta 22V Research, Michael Hirson ya fada, ganawar shugabannin biyu za ta zama rigakafin magance rikicin da babu wanda yake da muradin gani a tsakaninsu.

Sabanin Amurka da Sin ya karu a shekarun baya musamman a karkashin gwamnatin Trump sakamakon kare-karen haraji da kuma takunkuman fasaha a karkashin gwamnatin Biden.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai dai alaka ta fara kyautatuwa bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kai wata ziyara a birnin Beijing a watan Yuni, kana a farkon watan Oktoba, shugaban masu rinjaye na majalisar dattijan Amurka Chuck Schumer da wasu ’yan majalisar dattawan Amurka biyar dake wakiltar jam’iyyun Republican da Democrat, sun yi wata ganawa ta mintuna 80 da shugaba Xi Jinping.

“Dangantakar da ake gani a halin yanzu tsakanin Sin da Amurka ta sa duniya ta numfasa”, a cewar Shen Yamei, daraktan sashen nazarin Amurka, kuma abokiyar bincike a cibiyar nazarin kasa da kasa ta kasar Sin.

Kamar yadda Shugaba Xi ya sha nanatawa a baya kuma ya sake jaddada a yanzu, gasa mara tsafta a tsakanin manyan kasashen duniya ba ita ake yayi ba a wannan zamanin, a cewarsa, duniya tana da fadin da manyan kasashen biyu za su sakata su wahala cikin nasara. Don haka samun nasarar kowace kasa a tsakaninsu, wata dama ce ta ci gaba ga ’yar ’uwarta.

Abin sha’awa da kuma ke nuna shugabannin biyu sun hau turba guda, shi ma shugaba Biden ya sha alwashin cewa ba zai mayar da gasa a tsakanin kasashen biyu ta zama ta rikici ba, ya kuma yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa don tunkarar kalubalen duniya.

Wani abu dake kara nuna cewa Sinawa da Amurkawa na da kyakkyawar fatan cin moriyar juna shi ne, yadda sama da masu baje kolin Amurka 200 daga bangaren noma, na’urori masu sarrafa kwamfuta, na’urorin likitanci, motocin zamani masu aiki da sabbbin makamashi, kayan kwalliya, da dai sauransu suka halarci bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su na kasar Sin karo na shida (CIIE) da aka kammala kwanan nan a Shanghai. Ba a taba samun Amurkawa masu yawa da suka halarci bikin kamar a bana ba a tarihin bikin baje kolin.

A cewar bankin duniya, Amurka tana da karfin hada-hadar tattalin arziki na GDP na a kalla tiriliyan 25.5 a bara, yayin da na Sin ya kai kusan dala tiriliyan 17.9, wanda ya kai sama da kashi uku na tattalin arzikin duniya idan aka hade. Kasar Sin da Amurka suna da kusan kashi daya bisa hudu na al’ummar duniya, kuma cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya kai kusan kashi biyar na jimillar na duniya kaf.

Ba Amurka da Sin kawai idan dangantaka mai gwabi ta dore a tsakaninsu zai amfanar ba har da sauran kasashen duniya, kasancewar hakan za ta kara bude sabbin hanyoyin cinikayya musamman ganin cewa kasashen biyu ke da kashi daya bisa hudun yawan al’ummar duniya.

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana a jawabinsa na bude taron kasashen biyu a ranar Laraba, “akwai bukatar manyan kasashen su rika nuna cewa su manya ne a aikace” saboda hakan na da matukar muhimmanci ga samar da ci gaban duniya cikin hanzari da ba a ga irinsa ba cikin karni.

Muna fata zumunci ya dore tare da kauce wa komawa ’yar gidan jiya.( Abdulrazaq Yahuza)

Francisco
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Ba Ni Da Sha'awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba - Omorodion

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.