ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

by CGTN Hausa
3 years ago
Francisco

A halin yanzu kallo ya koma sabon babin da aka bude na kyautata alaka a tsakanin giwayen kasashen duniya biyu, Sin da Amurka yayin da aka yi ganawar keke-da-keke a tsakanin Shugaba Xi Jinping da takwaransa Joe Biden a birnin San Francisco na Amurka, ranar Laraba.

Bayan ganawar, shugabannin biyu sun jaddada muhimmancin dake akwai na dukkan kasashen duniya su mutunta juna da kuma samar da hanyar zama cikin lumana da barin kofofin sadarwa a bude tare da dakile rikici.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC
  • Wakilan Sin Da Kenya Sun Halarci Dandalin Tattaunawa Kan Hanyoyin Zamanintar Da Kasa

Sun amince da karfafa tattaunawa da hadin gwiwa a bangarori daban-daban, ciki har da kafa wata gamayya da za ta yi aiki kan yaki da muggan kwayoyi, da maido da manyan hanyoyin sadarwa na soja da kuma tinkarar matsalar sauyin yanayi tare.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban cibiyar bincike kan al’amuran kasar Sin ta 22V Research, Michael Hirson ya fada, ganawar shugabannin biyu za ta zama rigakafin magance rikicin da babu wanda yake da muradin gani a tsakaninsu.

Sabanin Amurka da Sin ya karu a shekarun baya musamman a karkashin gwamnatin Trump sakamakon kare-karen haraji da kuma takunkuman fasaha a karkashin gwamnatin Biden.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Sai dai alaka ta fara kyautatuwa bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kai wata ziyara a birnin Beijing a watan Yuni, kana a farkon watan Oktoba, shugaban masu rinjaye na majalisar dattijan Amurka Chuck Schumer da wasu ’yan majalisar dattawan Amurka biyar dake wakiltar jam’iyyun Republican da Democrat, sun yi wata ganawa ta mintuna 80 da shugaba Xi Jinping.

“Dangantakar da ake gani a halin yanzu tsakanin Sin da Amurka ta sa duniya ta numfasa”, a cewar Shen Yamei, daraktan sashen nazarin Amurka, kuma abokiyar bincike a cibiyar nazarin kasa da kasa ta kasar Sin.

Kamar yadda Shugaba Xi ya sha nanatawa a baya kuma ya sake jaddada a yanzu, gasa mara tsafta a tsakanin manyan kasashen duniya ba ita ake yayi ba a wannan zamanin, a cewarsa, duniya tana da fadin da manyan kasashen biyu za su sakata su wahala cikin nasara. Don haka samun nasarar kowace kasa a tsakaninsu, wata dama ce ta ci gaba ga ’yar ’uwarta.

Abin sha’awa da kuma ke nuna shugabannin biyu sun hau turba guda, shi ma shugaba Biden ya sha alwashin cewa ba zai mayar da gasa a tsakanin kasashen biyu ta zama ta rikici ba, ya kuma yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa don tunkarar kalubalen duniya.

Wani abu dake kara nuna cewa Sinawa da Amurkawa na da kyakkyawar fatan cin moriyar juna shi ne, yadda sama da masu baje kolin Amurka 200 daga bangaren noma, na’urori masu sarrafa kwamfuta, na’urorin likitanci, motocin zamani masu aiki da sabbbin makamashi, kayan kwalliya, da dai sauransu suka halarci bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su na kasar Sin karo na shida (CIIE) da aka kammala kwanan nan a Shanghai. Ba a taba samun Amurkawa masu yawa da suka halarci bikin kamar a bana ba a tarihin bikin baje kolin.

A cewar bankin duniya, Amurka tana da karfin hada-hadar tattalin arziki na GDP na a kalla tiriliyan 25.5 a bara, yayin da na Sin ya kai kusan dala tiriliyan 17.9, wanda ya kai sama da kashi uku na tattalin arzikin duniya idan aka hade. Kasar Sin da Amurka suna da kusan kashi daya bisa hudu na al’ummar duniya, kuma cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya kai kusan kashi biyar na jimillar na duniya kaf.

Ba Amurka da Sin kawai idan dangantaka mai gwabi ta dore a tsakaninsu zai amfanar ba har da sauran kasashen duniya, kasancewar hakan za ta kara bude sabbin hanyoyin cinikayya musamman ganin cewa kasashen biyu ke da kashi daya bisa hudun yawan al’ummar duniya.

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana a jawabinsa na bude taron kasashen biyu a ranar Laraba, “akwai bukatar manyan kasashen su rika nuna cewa su manya ne a aikace” saboda hakan na da matukar muhimmanci ga samar da ci gaban duniya cikin hanzari da ba a ga irinsa ba cikin karni.

Muna fata zumunci ya dore tare da kauce wa komawa ’yar gidan jiya.( Abdulrazaq Yahuza)

Francisco
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Ba Ni Da Sha'awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba - Omorodion

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.