ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar San Francisco: Tsaraba Daga Jawabin Shugaba Xi Kan Bukatar Sin Da Amurka Su Nuna Su Manya Ne A Aikace

by CGTN Hausa
3 years ago
Francisco

A halin yanzu kallo ya koma sabon babin da aka bude na kyautata alaka a tsakanin giwayen kasashen duniya biyu, Sin da Amurka yayin da aka yi ganawar keke-da-keke a tsakanin Shugaba Xi Jinping da takwaransa Joe Biden a birnin San Francisco na Amurka, ranar Laraba.

Bayan ganawar, shugabannin biyu sun jaddada muhimmancin dake akwai na dukkan kasashen duniya su mutunta juna da kuma samar da hanyar zama cikin lumana da barin kofofin sadarwa a bude tare da dakile rikici.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC
  • Wakilan Sin Da Kenya Sun Halarci Dandalin Tattaunawa Kan Hanyoyin Zamanintar Da Kasa

Sun amince da karfafa tattaunawa da hadin gwiwa a bangarori daban-daban, ciki har da kafa wata gamayya da za ta yi aiki kan yaki da muggan kwayoyi, da maido da manyan hanyoyin sadarwa na soja da kuma tinkarar matsalar sauyin yanayi tare.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban cibiyar bincike kan al’amuran kasar Sin ta 22V Research, Michael Hirson ya fada, ganawar shugabannin biyu za ta zama rigakafin magance rikicin da babu wanda yake da muradin gani a tsakaninsu.

Sabanin Amurka da Sin ya karu a shekarun baya musamman a karkashin gwamnatin Trump sakamakon kare-karen haraji da kuma takunkuman fasaha a karkashin gwamnatin Biden.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Sai dai alaka ta fara kyautatuwa bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kai wata ziyara a birnin Beijing a watan Yuni, kana a farkon watan Oktoba, shugaban masu rinjaye na majalisar dattijan Amurka Chuck Schumer da wasu ’yan majalisar dattawan Amurka biyar dake wakiltar jam’iyyun Republican da Democrat, sun yi wata ganawa ta mintuna 80 da shugaba Xi Jinping.

“Dangantakar da ake gani a halin yanzu tsakanin Sin da Amurka ta sa duniya ta numfasa”, a cewar Shen Yamei, daraktan sashen nazarin Amurka, kuma abokiyar bincike a cibiyar nazarin kasa da kasa ta kasar Sin.

Kamar yadda Shugaba Xi ya sha nanatawa a baya kuma ya sake jaddada a yanzu, gasa mara tsafta a tsakanin manyan kasashen duniya ba ita ake yayi ba a wannan zamanin, a cewarsa, duniya tana da fadin da manyan kasashen biyu za su sakata su wahala cikin nasara. Don haka samun nasarar kowace kasa a tsakaninsu, wata dama ce ta ci gaba ga ’yar ’uwarta.

Abin sha’awa da kuma ke nuna shugabannin biyu sun hau turba guda, shi ma shugaba Biden ya sha alwashin cewa ba zai mayar da gasa a tsakanin kasashen biyu ta zama ta rikici ba, ya kuma yi kira da a yi kokarin hadin gwiwa don tunkarar kalubalen duniya.

Wani abu dake kara nuna cewa Sinawa da Amurkawa na da kyakkyawar fatan cin moriyar juna shi ne, yadda sama da masu baje kolin Amurka 200 daga bangaren noma, na’urori masu sarrafa kwamfuta, na’urorin likitanci, motocin zamani masu aiki da sabbbin makamashi, kayan kwalliya, da dai sauransu suka halarci bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su na kasar Sin karo na shida (CIIE) da aka kammala kwanan nan a Shanghai. Ba a taba samun Amurkawa masu yawa da suka halarci bikin kamar a bana ba a tarihin bikin baje kolin.

A cewar bankin duniya, Amurka tana da karfin hada-hadar tattalin arziki na GDP na a kalla tiriliyan 25.5 a bara, yayin da na Sin ya kai kusan dala tiriliyan 17.9, wanda ya kai sama da kashi uku na tattalin arzikin duniya idan aka hade. Kasar Sin da Amurka suna da kusan kashi daya bisa hudu na al’ummar duniya, kuma cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya kai kusan kashi biyar na jimillar na duniya kaf.

Ba Amurka da Sin kawai idan dangantaka mai gwabi ta dore a tsakaninsu zai amfanar ba har da sauran kasashen duniya, kasancewar hakan za ta kara bude sabbin hanyoyin cinikayya musamman ganin cewa kasashen biyu ke da kashi daya bisa hudun yawan al’ummar duniya.

Kamar yadda Shugaba Xi ya bayyana a jawabinsa na bude taron kasashen biyu a ranar Laraba, “akwai bukatar manyan kasashen su rika nuna cewa su manya ne a aikace” saboda hakan na da matukar muhimmanci ga samar da ci gaban duniya cikin hanzari da ba a ga irinsa ba cikin karni.

Muna fata zumunci ya dore tare da kauce wa komawa ’yar gidan jiya.( Abdulrazaq Yahuza)

Francisco
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Ba Ni Da Sha'awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba - Omorodion

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.