• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Saki Fursunoni 3,898 Daga Gidan Gyaran Hali Saboda Rage Cinkoso A Gidan Yari

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
Ganduje

Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya saki adadin fursunoni dubu 3,898 daga gidajen gyara hali daban-daban da suke fadin jihar Kano domin rage cinkso a gidajen yarin a cikin shekaru bakwai da suka wuce.

Aikin sakin daurarrun wanda ya gudana a karkashin kwamitin jiha na afuwa da yafiya da aka sha yi a lokutan bukukuwa musamman irin lokacin Sallah. Fursunoni da dama sun ci albarkacin sallah inda suka samu ‘yanci daga dauri.

  • Tinubu Gogaggen Dan Siyasa Ne, In Ji Ganduje

Fursunoni 90 daga cikin 3,898 an sake su ne a jiya daga gidan yarin Gorondutse a cikin bukukuwan sallar Idin Layya da ya gudana.

Gwamnan ya sanar da sakin fursunoni 90 din ne a lokacin da ya ziyarci gidan yarin cikin bikin sallah, inda Gandujen ya bada tabbacin cigaba da yin kyawawan ayyukan da suka dace har zuwa karewar wa’adin mulkinsa a 2023.

A cewarsa, “Wannan aikin na gudana ne bisa bin umarcin Shugaban kasa Muhammadu Buhari na neman rage cinkoso a gidajen gyara halinmu.”

LABARAI MASU NASABA

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Gwamnan ya hori wadanda suka samu ‘yancin da su yi amfani da wannan damar wajen kyautata rayuwarsu na gaba tare da nemansu da su zama mutane na kwarai a cikin al’umma. Kazalika, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da samar da abubuwan da suka dace a jihar.

An gano fursunonin na nuna matukar murnarsu da lale bisa afuwar da suka samu a karkashin Gwamnatin jihar.

Wadanda aka saken sun sha alwashin canza dabi’unsu na da tare da yin abuhuwa masu kyau a cikin rayuwarsu.

A jawabinsa, Kwanturolan gidan yarin Kano, Sulaiman M Inuwa ya jinjina wa gwamnan bisa wannan kyawawan aikin alkairin da ya yi, “a tsawon shekaru na 30 da na yi ina aiki, ban taba ganin gwamnan da ya yi irin wannan ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Next Post
Buhari Zai Inganta Harkokin Tsaro Kafin Karshen Wa’adin Mulkinsa —Malami

Buhari Zai Inganta Harkokin Tsaro Kafin Karshen Wa'adin Mulkinsa —Malami

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.