• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Zai Sanya Hannu Kan Takardar Kashe Malamin Nan Da Ya Kashe Daliba Hanifa — Gwamnatin Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano, M. A. Lawal, ya ce, babu wani abun da zai dakatar da gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga ciki alkawarin da ya dauka na rattaba hannu kan takardar kisa ga makashin karamar daliba ‘yar shekara biyar, Hanifa da zarar aka kammala cika ka’idojin da shari’a ta gindaya.

Kwamishinan wanda yake magana kan mataki na gaba da gwamnatin jihar zata dauka kan matsayar hukuncin da mai shari’a, Usman Na’aba, ya yanke, ya yi bayanin cewa mutum biyun da aka yanke wa hukuncin kisan su na da damar daukaka kara cikin wata uku zuwa kotun gaba da Kotun da ta yanke musu hukunci.

“Kotu ta yanke wa mutum biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya, don haka gwamna ya yi alkawarin sanya hannu kan hukuncin kisa, don haka muna jiran kwanaki 90 su cika na damar daukaka kara kafin aiwatar da hakan,” Cewar Kwamishina.

Kwamishinan ya tabbatar da cewa alkawarin da suka yi tabbas a shirye suke su aiwatar amma dole su bi ka’idoji da matakan da shari’a ta ware wajen aiwatar da hakan.

Idan za ku iya tunawa dai Mai Shari’a Na’aba na babban kotun jihar Kano a makon jiya ya zartar da hukunci kan Tanko Abdulmalik, wanda ake zargi da kashe Hanifa, wanda kotun ta kama su dumu-dumu da laifin yin garkuwa da kashe karamar Dalian ‘yar shekara biyar a Kano wato Hanifa.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Inda kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar ratayewa har sai sun mutu.

Sannan kuma kotun ta yanke wa Abddulmalik da abokin aikata laifin nasa hukuncin shekara biyar a gidan kurkuku bisa sauran laifuka uku da ta samesu da aikatawa daga cikin tuhume-tuhumen da ake musu.

Kazalika, wacce ake zargi ta uku, Fatima Musa, kuma an yanke mata hukuncin shekara biyu a gidan gyara halinka bisa samunta da aikata babban laifi da kokarin yin garkuwa.

Antoni Janar din ya kara da cewa, “A cikin wata shida, Alkali ya kammala shari’ar. Wannan abun jinjina ne. Idan suka daukaka kara za mu sanar da jama’a cewa a shirye muke da hakan a kowani lokaci.

“Ga mutanen da suke ta jefa ayar tambaya kan ko shin za a aiwatar da hukuncin ko a’a, duk abun da zan ce shi ne doka dai doka ce kuma zamu jira kwanaki 90 din da suke da damar daukaka kara su yi.

Idan sun daukaka kara, shi kenan, nan da nan za mu dauki matakin hakan, idan kuma ba su daukaka kara ba har lokacin ya wuce gwamnati za ta aiwatar da abun da ya dace.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Umarci Wani Ma’aikacin Gwamanti Da Ya Dawo Da Albashinsa Na Shekara 11 A Filato

Next Post

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

29 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 hour ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

2 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

4 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

10 hours ago
Next Post
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.