• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Zai Sanya Hannu Kan Takardar Kashe Malamin Nan Da Ya Kashe Daliba Hanifa — Gwamnatin Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano, M. A. Lawal, ya ce, babu wani abun da zai dakatar da gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje daga ciki alkawarin da ya dauka na rattaba hannu kan takardar kisa ga makashin karamar daliba ‘yar shekara biyar, Hanifa da zarar aka kammala cika ka’idojin da shari’a ta gindaya.

Kwamishinan wanda yake magana kan mataki na gaba da gwamnatin jihar zata dauka kan matsayar hukuncin da mai shari’a, Usman Na’aba, ya yanke, ya yi bayanin cewa mutum biyun da aka yanke wa hukuncin kisan su na da damar daukaka kara cikin wata uku zuwa kotun gaba da Kotun da ta yanke musu hukunci.

“Kotu ta yanke wa mutum biyu hukuncin kisa ta hanyar rataya, don haka gwamna ya yi alkawarin sanya hannu kan hukuncin kisa, don haka muna jiran kwanaki 90 su cika na damar daukaka kara kafin aiwatar da hakan,” Cewar Kwamishina.

Kwamishinan ya tabbatar da cewa alkawarin da suka yi tabbas a shirye suke su aiwatar amma dole su bi ka’idoji da matakan da shari’a ta ware wajen aiwatar da hakan.

Idan za ku iya tunawa dai Mai Shari’a Na’aba na babban kotun jihar Kano a makon jiya ya zartar da hukunci kan Tanko Abdulmalik, wanda ake zargi da kashe Hanifa, wanda kotun ta kama su dumu-dumu da laifin yin garkuwa da kashe karamar Dalian ‘yar shekara biyar a Kano wato Hanifa.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Inda kotun ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar ratayewa har sai sun mutu.

Sannan kuma kotun ta yanke wa Abddulmalik da abokin aikata laifin nasa hukuncin shekara biyar a gidan kurkuku bisa sauran laifuka uku da ta samesu da aikatawa daga cikin tuhume-tuhumen da ake musu.

Kazalika, wacce ake zargi ta uku, Fatima Musa, kuma an yanke mata hukuncin shekara biyu a gidan gyara halinka bisa samunta da aikata babban laifi da kokarin yin garkuwa.

Antoni Janar din ya kara da cewa, “A cikin wata shida, Alkali ya kammala shari’ar. Wannan abun jinjina ne. Idan suka daukaka kara za mu sanar da jama’a cewa a shirye muke da hakan a kowani lokaci.

“Ga mutanen da suke ta jefa ayar tambaya kan ko shin za a aiwatar da hukuncin ko a’a, duk abun da zan ce shi ne doka dai doka ce kuma zamu jira kwanaki 90 din da suke da damar daukaka kara su yi.

Idan sun daukaka kara, shi kenan, nan da nan za mu dauki matakin hakan, idan kuma ba su daukaka kara ba har lokacin ya wuce gwamnati za ta aiwatar da abun da ya dace.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Umarci Wani Ma’aikacin Gwamanti Da Ya Dawo Da Albashinsa Na Shekara 11 A Filato

Next Post

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Related

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

57 minutes ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 hour ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

3 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

4 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

5 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

5 hours ago
Next Post
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.