• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gargaɗin Amurka Kan Nijeriya Na Tada Hankulan Masu Zuba Jari A Kasar – Minista

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gargaɗin da Amurka ta fitar kan Nijeriya ya na kawo babban cikas ga tattalin arzikin ƙasar.

Idris ya bayyana haka a lokacin da ya ke ganawa da manema labarai a ranar Litinin a Abuja.

  • Cin Zarafi: Kungiyoyin Kwadago Za Su Tsunduma Yajin Aiki A Ranar 14 Ga Nuwamba
  • Ka Nemi Sana’a Siyasa Ba Taka Ba Ce,Tinubu Ga Peter Obi

A ranar Juma’a, 3 ga Nuwamba, Ofishin Jakadancin Amurka da ke Abuja ya fitar da sanarwar “wata babbar barazana” ga manyan otal-otal da ke faɗin Nijeriya, amma ya ce jami’an tsaron Nijeriya na aiki tuƙuru domin daƙile barazanar.

Idris ya ce, “Abu mafi muhimmanci shi ne, kada a yi wa barazana fassara da cewa, ta mamaye dukkan faɗin ƙasar nan, domin yin hakan ba wani alheri ba ne.”

Amurka

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Ya ƙara da cewa, a kullum gwamnati ta na ɗaukar tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a da sauran dukkan maziyarta cikin ƙasar nan da muhimmanci.

Ya ce: “Mun fahimci damuwar da Amurka ke nunawa a cikin gargaɗin da ta fitar. Amma mun ga cewa, hakan bai kamata ba kuma bai dace a nuna wannan barazanar ta shafi dukkan otal-otal ɗin faɗin ƙasar nan ba.

“Abin da mu ka lura shi ne, yawancin wannan gargaɗin ba ya haifar da wani alheri, sai dai ya firgita mutane su tashi hankulansu. Sai kuma kawo illa ga tattalin arzikin ƙasa da gargaɗin ke yi. Sannan kuma ya kan zama wata hanyar yi wa ƙoƙarin da gwamnati ke yi na samun masu zuba jari a cikin ƙasa zagon ƙasa.

“A kullum mu na bayar da fifiko wajen kare rayuka da lafiyar duk wasu baƙin da su ka kawo ziyara cikin ƙasar nan.”

Amurka

Minista ya kuma rufe taron da bayyana irin nasarorin da jami’an tsaro su ka samu wajen daƙile matsalar tsaro a wasu jihohin ƙasar nan daban-daban a ‘yan kwanakin nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaBarazanar tsaroMinistan Yaɗa LabaraiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Karfafa Yaki Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Zamfara – Gwamna Lawal 

Next Post

Fashewar Tankar Gas Ce Sanadin Tashin Gobara A Ofishin Jakadancin Canada – FEMA

Related

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

38 minutes ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

3 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

5 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

8 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
Fashewar Tankar Gas Ce Sanadin Tashin Gobara A Ofishin Jakadancin Canada – FEMA

Fashewar Tankar Gas Ce Sanadin Tashin Gobara A Ofishin Jakadancin Canada - FEMA

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.