• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garin Kwakin Da Ake Sarrafawa A Yankin Ugep Ya Janyo Takaddama

by Abubakar Abba
3 years ago
Garin Kwaki

Cacar-baki ta barke tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin sarrafa rogo zuwa garin kwaki da ake kira da Ugep ‘Garri’. Ugep ‘Garri’, ana sarrafa shi ne a garin Ugep da ke a karamar hukumar Yakur a jihar Koros Ribas.

Musayar yawun a tsakanin masu ruwa da tsakanin a fannin ta kaure ne biyo bayan furucin da shugaban kungiyar masu sarrafa Garin Kwaki reshen jihar (CGAN), Mista Augustine Okua ya yi na gargadin al’ummar da ke Kudancin Nijeriya, da na kasa baki daya ma cewa su guji shan Garin Kwakin da ake sarrafa wa a yankin na Ugep.

  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 
  • Harin Jirgin Kaduna-Abuja: Hukumar Jiragen Kasa Ta Yi Asarar Miliyan 53 A Cikin Watanni 5

A wata hira da Augustine ya yi zargin cewa, garin shan zai iya shafar kiwon lafiyar jama’ar da suka sha shi, ganin cewa, wasu masu sarrafa rogo a yankin zuwa Garin Kwaki suna yi a cikin gaggawa ba tare sun bar rogon ya gama tsanewa ba don kawai su samu kudi da wuri.

Ya ce, Gari na dauke da sanadarin cyanide masu nauyin gaske wanda kuma zai iya shafar kiwon lafiyar wanda ya yi amfani da shi ko kuma ya jawo mutuwar wanda ya yi amfani da su, inda ya yi nuni da cewa, akalla ya fi da cewa a bar rogon ya kai kwana uku kafin a fara soya shi don mayar da shi gari.

Sai dai, wannan kalaman na Augustine, bai yi wa sauran masu ruwa da tsaki a fannin daga ke a jihar dadi ba, inda wasun su suka mayar masa da kakkausar martani.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Wasu daga cikinsu, sun ce, Augustine ya yi furucin ne saboda gonarsa ta noman Rogo karamace, inda a yanzu ya ke son zama mai sarrafa gari, hakan kuma ya sa yake son ya tsorata ‘ yan Nijeriya da sauran masu yin amfani da shi da ake sarrafa wa a garin na Ugep.

Cif Okoi Obono-Obla, tsohon mai bai wa shugaba Muhammadu Buhari shawara kuma basarake a garin na Ugep, shi ma ya soki furucin na Augustine, inda ya ce Augustine na kawai son bata wa garin suna ne da kuma son hana wa samun Garin karbuwa a gun jama’a.

Ya ce, kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa shi zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan Garin da ake sarrafa wa a garin ba.

Ya kara da cewa, kamata ya yi kafin ya yi furucin ya faga da jin ra’ayoyin ta alummar Ugep da kuma sauran masu sarrafa rogon.

“Kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa rogo zuwa zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan garin da ake sarrafa wa a garin ba”.

Ya yi nuni da cewa, garin da ake sarrafa wa a yankin shi ne ya fi kyau a daukacin fadin kasar nan.

Shi ma Yariman yankin Mkpani Oka Ibor ya sanar da cewa, furucin na Augustine son nuna gawawar alummar garin ne da kuma bata masu suna, musamman manyan masu sarrfara rogo zuwa gari a garin.

Sai dai, wani masani a fannin sarrafa rogo zuwa gari a yankin Mike Kit Oka ya sanar da cewa, rogo na dauke da sanadarin cyanide kadan ne, sabanin sanadarin na cyanide da ke jikin sauran amfanin gona.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025
Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.