ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garin Kwakin Da Ake Sarrafawa A Yankin Ugep Ya Janyo Takaddama

by Abubakar Abba
4 years ago
Garin Kwaki

Cacar-baki ta barke tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin sarrafa rogo zuwa garin kwaki da ake kira da Ugep ‘Garri’. Ugep ‘Garri’, ana sarrafa shi ne a garin Ugep da ke a karamar hukumar Yakur a jihar Koros Ribas.

Musayar yawun a tsakanin masu ruwa da tsakanin a fannin ta kaure ne biyo bayan furucin da shugaban kungiyar masu sarrafa Garin Kwaki reshen jihar (CGAN), Mista Augustine Okua ya yi na gargadin al’ummar da ke Kudancin Nijeriya, da na kasa baki daya ma cewa su guji shan Garin Kwakin da ake sarrafa wa a yankin na Ugep.

  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 
  • Harin Jirgin Kaduna-Abuja: Hukumar Jiragen Kasa Ta Yi Asarar Miliyan 53 A Cikin Watanni 5

A wata hira da Augustine ya yi zargin cewa, garin shan zai iya shafar kiwon lafiyar jama’ar da suka sha shi, ganin cewa, wasu masu sarrafa rogo a yankin zuwa Garin Kwaki suna yi a cikin gaggawa ba tare sun bar rogon ya gama tsanewa ba don kawai su samu kudi da wuri.

ADVERTISEMENT

Ya ce, Gari na dauke da sanadarin cyanide masu nauyin gaske wanda kuma zai iya shafar kiwon lafiyar wanda ya yi amfani da shi ko kuma ya jawo mutuwar wanda ya yi amfani da su, inda ya yi nuni da cewa, akalla ya fi da cewa a bar rogon ya kai kwana uku kafin a fara soya shi don mayar da shi gari.

Sai dai, wannan kalaman na Augustine, bai yi wa sauran masu ruwa da tsaki a fannin daga ke a jihar dadi ba, inda wasun su suka mayar masa da kakkausar martani.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Wasu daga cikinsu, sun ce, Augustine ya yi furucin ne saboda gonarsa ta noman Rogo karamace, inda a yanzu ya ke son zama mai sarrafa gari, hakan kuma ya sa yake son ya tsorata ‘ yan Nijeriya da sauran masu yin amfani da shi da ake sarrafa wa a garin na Ugep.

Cif Okoi Obono-Obla, tsohon mai bai wa shugaba Muhammadu Buhari shawara kuma basarake a garin na Ugep, shi ma ya soki furucin na Augustine, inda ya ce Augustine na kawai son bata wa garin suna ne da kuma son hana wa samun Garin karbuwa a gun jama’a.

Ya ce, kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa shi zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan Garin da ake sarrafa wa a garin ba.

Ya kara da cewa, kamata ya yi kafin ya yi furucin ya faga da jin ra’ayoyin ta alummar Ugep da kuma sauran masu sarrafa rogon.

“Kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa rogo zuwa zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan garin da ake sarrafa wa a garin ba”.

Ya yi nuni da cewa, garin da ake sarrafa wa a yankin shi ne ya fi kyau a daukacin fadin kasar nan.

Shi ma Yariman yankin Mkpani Oka Ibor ya sanar da cewa, furucin na Augustine son nuna gawawar alummar garin ne da kuma bata masu suna, musamman manyan masu sarrfara rogo zuwa gari a garin.

Sai dai, wani masani a fannin sarrafa rogo zuwa gari a yankin Mike Kit Oka ya sanar da cewa, rogo na dauke da sanadarin cyanide kadan ne, sabanin sanadarin na cyanide da ke jikin sauran amfanin gona.

Garin Kwaki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.