ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garin Kwakin Da Ake Sarrafawa A Yankin Ugep Ya Janyo Takaddama

by Abubakar Abba
4 years ago
Garin Kwaki

Cacar-baki ta barke tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin sarrafa rogo zuwa garin kwaki da ake kira da Ugep ‘Garri’. Ugep ‘Garri’, ana sarrafa shi ne a garin Ugep da ke a karamar hukumar Yakur a jihar Koros Ribas.

Musayar yawun a tsakanin masu ruwa da tsakanin a fannin ta kaure ne biyo bayan furucin da shugaban kungiyar masu sarrafa Garin Kwaki reshen jihar (CGAN), Mista Augustine Okua ya yi na gargadin al’ummar da ke Kudancin Nijeriya, da na kasa baki daya ma cewa su guji shan Garin Kwakin da ake sarrafa wa a yankin na Ugep.

  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 
  • Harin Jirgin Kaduna-Abuja: Hukumar Jiragen Kasa Ta Yi Asarar Miliyan 53 A Cikin Watanni 5

A wata hira da Augustine ya yi zargin cewa, garin shan zai iya shafar kiwon lafiyar jama’ar da suka sha shi, ganin cewa, wasu masu sarrafa rogo a yankin zuwa Garin Kwaki suna yi a cikin gaggawa ba tare sun bar rogon ya gama tsanewa ba don kawai su samu kudi da wuri.

ADVERTISEMENT

Ya ce, Gari na dauke da sanadarin cyanide masu nauyin gaske wanda kuma zai iya shafar kiwon lafiyar wanda ya yi amfani da shi ko kuma ya jawo mutuwar wanda ya yi amfani da su, inda ya yi nuni da cewa, akalla ya fi da cewa a bar rogon ya kai kwana uku kafin a fara soya shi don mayar da shi gari.

Sai dai, wannan kalaman na Augustine, bai yi wa sauran masu ruwa da tsaki a fannin daga ke a jihar dadi ba, inda wasun su suka mayar masa da kakkausar martani.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Wasu daga cikinsu, sun ce, Augustine ya yi furucin ne saboda gonarsa ta noman Rogo karamace, inda a yanzu ya ke son zama mai sarrafa gari, hakan kuma ya sa yake son ya tsorata ‘ yan Nijeriya da sauran masu yin amfani da shi da ake sarrafa wa a garin na Ugep.

Cif Okoi Obono-Obla, tsohon mai bai wa shugaba Muhammadu Buhari shawara kuma basarake a garin na Ugep, shi ma ya soki furucin na Augustine, inda ya ce Augustine na kawai son bata wa garin suna ne da kuma son hana wa samun Garin karbuwa a gun jama’a.

Ya ce, kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa shi zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan Garin da ake sarrafa wa a garin ba.

Ya kara da cewa, kamata ya yi kafin ya yi furucin ya faga da jin ra’ayoyin ta alummar Ugep da kuma sauran masu sarrafa rogon.

“Kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa rogo zuwa zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan garin da ake sarrafa wa a garin ba”.

Ya yi nuni da cewa, garin da ake sarrafa wa a yankin shi ne ya fi kyau a daukacin fadin kasar nan.

Shi ma Yariman yankin Mkpani Oka Ibor ya sanar da cewa, furucin na Augustine son nuna gawawar alummar garin ne da kuma bata masu suna, musamman manyan masu sarrfara rogo zuwa gari a garin.

Sai dai, wani masani a fannin sarrafa rogo zuwa gari a yankin Mike Kit Oka ya sanar da cewa, rogo na dauke da sanadarin cyanide kadan ne, sabanin sanadarin na cyanide da ke jikin sauran amfanin gona.

Garin Kwaki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.