Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana gasar wasanni ta kasa karo na 22 mai taken “Gateway Games 2024” wadda ake gudanarwa yanzu haka a birnin Abeokuta na jihar Ogun, a matsayin wata hanya dake hada kan matasa da kuma zakulo masu hazaka a bangarori da dama.
A ranar Alhamis ne aka kammala babbar gasar wasanni ta shekara-shekara, wadda ta kunshi ‘yan wasa sama da 10,000 daga sassan Nijeriya, wacce jihar Delta ta zama zakara a karo na biyar a jere.
- ‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano
- Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
A cikin wani jawabi da ya yi ta wayar tarho, Obasanjo ya bayyana cewa, gasar Gateway ta kasance abin tunatarwa ga yan Nijeriya cewa kowane matashi yana da damar nuna bajintar shi da kuma kwazonshi akan abinda ya saka a gaba.
“Ina isar da wannan sakon ba wai a matsayina na tsohon shugaban kasa ba, har ma a matsayina na dan jihar Ogun cike da alfahari, na kasance tare da ku a lokacin bikin bude gasar, na kalli wasannin a cikin dakina, kuma hakika wasannin sun nuna cewa ba wai kawai wasanni ba ne, alama ce ta hadin kai, baje kolin hazaka, da kuma kishin kasa.
“Daga karshe Obasanjo ya jinjinawa jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya, da kuma kananan kungiyoyin da aka gayyata bisa jajircewarsu, inda ya kara da cewa, kwamitocin da suka shirya gasar, abokan hadin gwiwa, da masu aikin sa kai na hukumar wasanni ta kasa sun cancanci a yaba musu saboda mayar da wannan mafarkin da ya zama gaskiya.” In ji Obasanjo
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp