• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

by Rabilu Sanusi Bena
3 weeks ago
in Nishadi
0
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin masu shirya fina-finai a masana’antar Kannywood, Darakta kuma jarumi a masana’antar; Falau A. Dorayi ya yi karin haske dangane da yadda ya kamata masana’antar ta mayar da hankalin, duba da cewa; yanzu kida ya canza, don haka; rawa ma ta canza. 

A cewar Dorayi, an matukar samun sauyi a wannan masana’anta, ta fuskar samun kudade; ba kamar da ba. A wata hira da ya yi da RFI Hausa, Falalu ya bayyana cewa; ya fara fim tsawon shekaru da dama da suka shude, inda ya bayyana cewa; duba da yawaitar gidajen Gala a fadin Nijeriya, ya sa yake ganin wannan ita kadai hanya mafi bullewa.

  • INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

“Duk da cewa, har yanzu masana’antar ta Kannywood babu laifi; ana samun kudade, amma dai akwai bukatar a fadada hanyoyin samun kudaden shiga a masana’antar, wanda kuma a halin yanzu babu wata hanya da ta fi nuna fina-finai a gidajen Galar, yanzu haka; idan ba don samun tashar ‘Youtube’ da aka yi ba, da ba a nsan yadda masana’antar za ta kasance ba”, in ji shi.

Ya kara da cewa, misali akwai daruruwan masu sana’ar ‘downloading’ a Arewacin Nijeriya, amma kwata-kwata abin da suke biya bai fi Naira miliyan daya zuwa biyu ba, sannan kuma ba kowa ne ke iya saka data ya kalli fim a shafukan yanar gizo ba, kowa ya fi son idan abokinsa ko kawarta ta dauko; sai ya tura masa ko ta tura mata ba tare da sun kashe ko sisi ba, kazalika kuma a ‘YouTube’ ne kadai wanda ya dauki nauyin fim zai iya dan samun wani abu mai dama-dama, idan an kalla.

“Tun lokacin da aka daina buga faifan CD a masana’antar Kannywood, samun kudade ya ja baya, amma yanzu ake neman hanyoyin da za a bi, domin warware wadannan matsaloli, don haka a ganina; kamata ya yi a dawo inda aka bari, tunda har aka gano cewa; masu sha’awar kallon fina-finan Hausa, za su iya zuwa gidajen Gala tun daga karfe biyar na yamma zuwa lokacin sallar Magriba, sannan kuma su sake dawowa daga karfe 8 zuwa 12 na dare, su biya kudi don kallon fina-finan da ake haskawa a wadannan wurare, me zai hana mu mayar da akalarmu zuwa wajensu?” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

“Ni na san fina-finan da aka haska a gidajen Gala da aka samu fiye da Naira miliyan daya a rana daya, wasu kuma har miliyan biyu, yanzu idan ka duba tun daga Kano har Nijar za ka dinga ganin gidajen Gala, haka zalika daga nan Kano har zuwa birnin Legas ma akwai su, saboda haka; me zai hana mu rika amfani da wannan dama wajen fadada adadin kudaden shiga da wannan masana’anta mai albarka take samu?

Daga karshe, ya bukaci hadin kai daga dukkanin wasu masu ruwa da tsaki, wajen ganin wannan haka ya cimma ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gala
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Next Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Related

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

2 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

3 weeks ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

4 weeks ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

2 months ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

2 months ago
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri'ar Jin Ra'ayin Jama'a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.