• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bayan garin birnin Addis Ababa na kasar Habasha, akwai jerin wasu gine-gine masu salo na musamman, wadanda suke matukar jan hankalin al’umma, kuma su ne gine-ginen hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka(Africa CDC) wadanda aka kammala gina su a kwanan baya, wadanda kuma suka mai da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka a matsayin daya daga cikin cibiyoyin kandagarkin cututtuka mafiya ci gaba da zamaninta a duniya. Kasar Sin ce ta samar da gudummawar gina shi, matakin da ya sa cibiyar ta zama ta biyu bayan cibiyar taron kungiyar tarayyar Afirka, wadda ita ma kasar Sin ce ta gina.

Afirka nahiya ce da aka fi samun kasashe masu tasowa, inda har yanzu ake fuskantar matsalolin kiwon lafiya, musamman ma sakamakon yaduwar annobar Covid-19, ya zama dole a gaggauta aikin gina tsarin kandagarkin cututtuka ta nahiyar. Yadda aka kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka a Afirka, babu shakka zai inganta karfin kasashen na kandagarkin cututtuka.

Mista Charles Onunaiju, masanin ilmin huldar kasa da kasa na Nijeriya, wanda kuma shi ne darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin a Nijeriya, yayin da ya tattauna da dan jarida a kwanan baya ya bayyana cewa, “Kasar Sin ta cika alkawarin da ta dauka na fara samar da kasashen Afirka rigakafin cutar Covid-19 da zarar ta kammala nazari da harhada rigakafin, ta kuma sanar da fara aikin gina cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka kafin lokacin da aka tsai da, ga shi kuma ta kammla aikin yadda ya kamata, kyaun alkawari cikawa, kuma duk wadannan sun shaida kasar Sin kasa ce mai rikon amana. Yanzu kuma ina da imanin cewa, batun gina al‘ummar Sin da Afirka mai Koshin lafiya ba batu ne na fatar Baki ba.”

Daidai kamar yadda mista Onunaiju ya fada, tun bayan bullar cutar Covid-19 a Afirka a shekarar 2020, nan da nan kasar Sin ta samar da gudummawarta, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci taron hadin kan Sin da Afirka kan yaki da cutar Covid-19, inda ya gabatar da manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, kuma kawo yanzu, kasar Sin ta samar da rigakafi sama da miliyan 189 ga kasashen Afirka sama da 50, baya ga yadda ta yi kokarin aiwatar da hadin gwiwa da Masar da dai sauran kasashen Afirka, don kasashen su samu kwarewar samar da rigakafin da kansu. Ban da wannan, kasar Sin ta kuma tura tawagogin masana ilmin kiwon lafiya 5 da kuma kungiyoyin ma’aikatan lafiya 46 zuwa kasashen Afirka don su ba da taimako wajen dakile cutar a Afirka. Ga shi yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka tare da mika ta hannun kungiyar tarayyar Afirka.

Daga wannan sabon mafari, muna fatan za a kara cimma sabbin ci gaba ta fannin ayyukan kiwon lafiya a kasashen Afirka bisa ga manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, don ta kasance laimar da ke kare al’ummomin kasashen Afirka daga cututtuka.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Sin Ta Kawo wa Duniya Cikin Shekaru 3 Da Ta Shafe Tana Kokarin Tinkarar Cutar COVID-19

Next Post

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

49 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

2 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

3 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

15 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

19 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

20 hours ago
Next Post
Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.