• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bayan garin birnin Addis Ababa na kasar Habasha, akwai jerin wasu gine-gine masu salo na musamman, wadanda suke matukar jan hankalin al’umma, kuma su ne gine-ginen hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka(Africa CDC) wadanda aka kammala gina su a kwanan baya, wadanda kuma suka mai da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka a matsayin daya daga cikin cibiyoyin kandagarkin cututtuka mafiya ci gaba da zamaninta a duniya. Kasar Sin ce ta samar da gudummawar gina shi, matakin da ya sa cibiyar ta zama ta biyu bayan cibiyar taron kungiyar tarayyar Afirka, wadda ita ma kasar Sin ce ta gina.

Afirka nahiya ce da aka fi samun kasashe masu tasowa, inda har yanzu ake fuskantar matsalolin kiwon lafiya, musamman ma sakamakon yaduwar annobar Covid-19, ya zama dole a gaggauta aikin gina tsarin kandagarkin cututtuka ta nahiyar. Yadda aka kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka a Afirka, babu shakka zai inganta karfin kasashen na kandagarkin cututtuka.

Mista Charles Onunaiju, masanin ilmin huldar kasa da kasa na Nijeriya, wanda kuma shi ne darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin a Nijeriya, yayin da ya tattauna da dan jarida a kwanan baya ya bayyana cewa, “Kasar Sin ta cika alkawarin da ta dauka na fara samar da kasashen Afirka rigakafin cutar Covid-19 da zarar ta kammala nazari da harhada rigakafin, ta kuma sanar da fara aikin gina cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka kafin lokacin da aka tsai da, ga shi kuma ta kammla aikin yadda ya kamata, kyaun alkawari cikawa, kuma duk wadannan sun shaida kasar Sin kasa ce mai rikon amana. Yanzu kuma ina da imanin cewa, batun gina al‘ummar Sin da Afirka mai Koshin lafiya ba batu ne na fatar Baki ba.”

Daidai kamar yadda mista Onunaiju ya fada, tun bayan bullar cutar Covid-19 a Afirka a shekarar 2020, nan da nan kasar Sin ta samar da gudummawarta, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci taron hadin kan Sin da Afirka kan yaki da cutar Covid-19, inda ya gabatar da manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, kuma kawo yanzu, kasar Sin ta samar da rigakafi sama da miliyan 189 ga kasashen Afirka sama da 50, baya ga yadda ta yi kokarin aiwatar da hadin gwiwa da Masar da dai sauran kasashen Afirka, don kasashen su samu kwarewar samar da rigakafin da kansu. Ban da wannan, kasar Sin ta kuma tura tawagogin masana ilmin kiwon lafiya 5 da kuma kungiyoyin ma’aikatan lafiya 46 zuwa kasashen Afirka don su ba da taimako wajen dakile cutar a Afirka. Ga shi yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka tare da mika ta hannun kungiyar tarayyar Afirka.

Daga wannan sabon mafari, muna fatan za a kara cimma sabbin ci gaba ta fannin ayyukan kiwon lafiya a kasashen Afirka bisa ga manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, don ta kasance laimar da ke kare al’ummomin kasashen Afirka daga cututtuka.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Sin Ta Kawo wa Duniya Cikin Shekaru 3 Da Ta Shafe Tana Kokarin Tinkarar Cutar COVID-19

Next Post

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

6 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

9 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.