Gobara ta tashi a wani gidan mai da ke kan titin Old Akute, a unguwar Obawole a Iju Ishaga, da ke ƙaramar hukumar Ifako-Ijaiye a Jihar Legas.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA) ta tabbatar da afkuwar gobarar, wadda ta fara ne da misalin ƙarfe 4 na yammacin ranar Laraba.
- Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki
- Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka
Wasu shaidu sun ce sun ji ƙarar fashewa mai ƙarfi, wanda ya jawo hankalin mazauna unguwar da masu wucewa.
Jubril Gawat, mai bai wa Gwamna Babajide Sanwo-Olu shawara kan kafafen sada zumunta, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce jami’an hukumar kashe gobara sun isa wajen cikin gaggawa.
A cewarsa, gobarar na iya kasancewa ta samo asali ne daga wani gini da ke bayan gidan man.
Rahotanni sun nuna cewa gobarar na iya tashi ne daga tankunan mai da ke ƙasa, kafin ta bazu zuwa cikin gidan man gaba ɗaya.
Hukumar kashe gobara ta jihar ta yi gaggawar killace wajen domin hana cunkoso da tabbatar da tsaron jama’a yayin aikin kashe gobarar.
Mai magana da yawun hukumar kashe gobarar, Shakiru Amodu, ya tabbatar da cewa an samu nasarar kashe gobarar kafin ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.
Kafin ƙarfe 6 na yamma, jami’an agajin gaggawa sun shawo kan lamarin gaba ɗaya, tare da killace yankin da abin ya shafa domin kaucewa wata barazana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp