Barkanku da kasancewa tare da shafin GORON JUMA’A shafin dake bawa kowa damar mika sakon gaishe-gaishensa zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki, na kusa dana nesa har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba. Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu sakonnin gaishe-gaishen da ku ka aiko mana, inda sakon farko ya fara da cewa;
- GORON JUMA’A 28-03-2025
- Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar SinÂ
Sako Daga Zaina Ibrahim Lawan Jihar Katsina:
Ina gaishe da Zuhra Abdulkadir, Karima Yusuf, Zainab Baba (Namesake) Aisha Isma’il, Binta Ahmad, da sauran kawayenmu da ban ambaci sunansu ba.
Sako daga Al’amin Mubarak Ahmad:
Ina gaishe da mahaifiyata Hajiya Zuwairiyya da mahaifina Alhaji Mubarek Ahmad, sannan ina gaishe da kanwar mahaifiyata Anti Luba, da Yayata Anti Fatima da Anti Maryam da sauran kannenta.Â
Sako daga Bilal Salisu Gabasawa:
Ina so a mikan sakon gaiswa ta zuwa ga masoyiya Habiba, abar kaunata in sha Allah har karshen rayuwa, da fatan ta yi juma’a lafiya.
Sako daga Suwaiba Lawan Jihar Kano:
Ina so a gaishe mun da mahaifana da kuma.mijina uban ‘ya’yana daya tamkar ya dubu rabin raina Nasir Muhd, Allah ya sa sakon ya isa gare shi, ina yi muku fatan alkhairi.
Sako daga Abba Ahmad Kaduna:
Ina gaishe da mahaifina da kuma mahaifiya ta, ina gaishe da kannena; Momi, ikram, sadiya, hafsa, sadik, sannan ina gaishe da duk kanin al’ummar musulmi bakidaya, Allah ya sa mu yi juma’a lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp