• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 29 ga watan Mayu ne aka yi bikin ranar jami’an wanzar da zaman lafiya ta MDD na bana. Kudiri mai lamba 57/129 na babban taron MDD ne ya ayyana wannan rana a ranar 11 ga watan Disamban, shekarar 2002.

Bayanai na nuna cewa, an gudanar da aikin tabbatar da zaman lafiya na MDD na farko a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1948, lokacin da kwamitin sulhun MDD ya amince da tura wata karamar tawagar sojoji zuwa yankin gabas ta tsakiya a matsayin masu sanya ido kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Isra’ila da kasashen Larabawa dake makwabtaka da ita.

  • An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

Kasar Sin ita ce kasa ta biyu dake biyan kudin tallafi da kudin karo karo ga MDD yadda ya kamata, kuma ita ce kasar da ta fi kowacce ba da adadi mai yawa na dakarun wanzar da zaman lafiya, tun daga shekarar 1990.

Haka kuma, Sin ta aike da dakarun da yawansu ya kai sama da dubu 50, cikin shekaru 30 da suka gabata. Dakarun wanzar da zaman lafiya na kasar Sin suna gudanar da ayyukan daidaita rikici da kiyaye kwanciyar hankali da kuma ingiza ci gaban tattalin arziki a kasashe da yankuna sama da 20, ciki har da Cambodiya, da Kongo(Kinshasa), da Liberiya, da Sudan, da Lebanon, da Sudan ta kudu, da Mali, da Afirka ta tsakiya da sauransu.

A halin yanzu, jami’an wanzar da zaman lafiya na kasar Sin sama da 2500 suna ci gaba da gudanar da ayyuka a wurare daban-daban da kuma hedkwatar MDD. Wannan ya kara shaida kudirin kasar na neman ganin zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ci gaba sun samu a duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

A yayin da ake amfani da wannan rana, wajen tuna gudummawar da masu kayan sarki da fararen hula, wadanda suka kwanta dama yayin da suke aikin wanzar da zaman lafiya, mataimakin babban sakataren MDD mai kula da harkokin kiyaye zaman lafiya Jean-Pierre François Renaud Lacroix ya bayyana cewa, yana alfahari sosai da yadda aka gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD har na tsawon shekaru 75, kana ya yabawa kasar Sin kan yadda ta samar da muhimmiyar gudummawa ga sha’anin kiyaye zaman lafiya na MDD.

Jean-Pierre Lacroix ya ce, Sin ta kasance mai goyon bayan MDD wajen gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya, kana ta samar da gudummawa sosai ga ayyukan. Ya kuma bayyana cewa, kasashe da dama sun samu zaman lafiya da kwanciyar hankali sanadiyyar ayyukan kiyaye zaman lafiya, lamarin da ya shaida cewa, ayyukan suna da amfani.

Don haka, yana fatan a nan gaba, MDD da Sin za su kara hadin gwiwa kan ayyukan kiyaye zaman lafiya. Abubuwan da Sin take gudanarwa abu ne da ake ganinsu a zahiri ba maganar fatar baki ba. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Next Post

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Related

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

13 hours ago
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

14 hours ago
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

15 hours ago
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

17 hours ago
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

18 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

2 days ago
Next Post
Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.