• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gudummawar Kasar Sin Ga Aikin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya Abu Ne Da Ake Gani A Zahiri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 29 ga watan Mayu ne aka yi bikin ranar jami’an wanzar da zaman lafiya ta MDD na bana. Kudiri mai lamba 57/129 na babban taron MDD ne ya ayyana wannan rana a ranar 11 ga watan Disamban, shekarar 2002.

Bayanai na nuna cewa, an gudanar da aikin tabbatar da zaman lafiya na MDD na farko a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1948, lokacin da kwamitin sulhun MDD ya amince da tura wata karamar tawagar sojoji zuwa yankin gabas ta tsakiya a matsayin masu sanya ido kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Isra’ila da kasashen Larabawa dake makwabtaka da ita.

  • An Gudanar Da Taro Karo Na 12 Na Dandalin Masanan Sin Da Afirka

Kasar Sin ita ce kasa ta biyu dake biyan kudin tallafi da kudin karo karo ga MDD yadda ya kamata, kuma ita ce kasar da ta fi kowacce ba da adadi mai yawa na dakarun wanzar da zaman lafiya, tun daga shekarar 1990.

Haka kuma, Sin ta aike da dakarun da yawansu ya kai sama da dubu 50, cikin shekaru 30 da suka gabata. Dakarun wanzar da zaman lafiya na kasar Sin suna gudanar da ayyukan daidaita rikici da kiyaye kwanciyar hankali da kuma ingiza ci gaban tattalin arziki a kasashe da yankuna sama da 20, ciki har da Cambodiya, da Kongo(Kinshasa), da Liberiya, da Sudan, da Lebanon, da Sudan ta kudu, da Mali, da Afirka ta tsakiya da sauransu.

A halin yanzu, jami’an wanzar da zaman lafiya na kasar Sin sama da 2500 suna ci gaba da gudanar da ayyuka a wurare daban-daban da kuma hedkwatar MDD. Wannan ya kara shaida kudirin kasar na neman ganin zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ci gaba sun samu a duniya baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

A yayin da ake amfani da wannan rana, wajen tuna gudummawar da masu kayan sarki da fararen hula, wadanda suka kwanta dama yayin da suke aikin wanzar da zaman lafiya, mataimakin babban sakataren MDD mai kula da harkokin kiyaye zaman lafiya Jean-Pierre François Renaud Lacroix ya bayyana cewa, yana alfahari sosai da yadda aka gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD har na tsawon shekaru 75, kana ya yabawa kasar Sin kan yadda ta samar da muhimmiyar gudummawa ga sha’anin kiyaye zaman lafiya na MDD.

Jean-Pierre Lacroix ya ce, Sin ta kasance mai goyon bayan MDD wajen gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya, kana ta samar da gudummawa sosai ga ayyukan. Ya kuma bayyana cewa, kasashe da dama sun samu zaman lafiya da kwanciyar hankali sanadiyyar ayyukan kiyaye zaman lafiya, lamarin da ya shaida cewa, ayyukan suna da amfani.

Don haka, yana fatan a nan gaba, MDD da Sin za su kara hadin gwiwa kan ayyukan kiyaye zaman lafiya. Abubuwan da Sin take gudanarwa abu ne da ake ganinsu a zahiri ba maganar fatar baki ba. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafin Mai: Ba A Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da NLC Ba

Next Post

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Related

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

7 hours ago
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
Daga Birnin Sin

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

9 hours ago
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

12 hours ago
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

13 hours ago
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

1 day ago
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

1 day ago
Next Post
Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

Sin Na Son Hadin Kai Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Nazarin Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.