• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kowane lokaci, ilimi na samun tagomashi da kuma girmamawa daga wurin al’umma. Masu ilimi, su ne ke samun ingantacciyar rayuwa, wadda kowa da kowa ke sha’awa ko mararin samun irin ta.

Idan mutane suka karanci bangaren fannonin da ake ribibin su wajen daukar ma’aikata, ko shakka babu suna samun albashi mai matukar tsoka, ta yadda za su taimaki kansu da iyayensu da sauran danginsu baki-daya.

  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma
  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano

Har ila yau, ilimi na sa a samu daukaka; wadda ba a taba zato ba, sannan yana taimakawa wajen cimma kowane irin buri na rayuwa.

Bugu da kari, ilimi na bayar da dama wajen samun kudaden da za su taimaka wa mutum a rayuwarsa ta yau da kullum tare kuma da samun farin ciki ta fuskoki daban-daban.

6- Masu Ilimi Na Matukar Taimaka Wa Al’umma 

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Ta wace hanya masu ilimi ke taimaka wa al’umma? Kasancewar masu ilimi, sun san muhimmancinsa tare kuma da sanin abin da ya kamata, shi yasa a duk inda suka fi yawa ake samun zaman lafiya da hadin kai da kuma rayuwa mai inganci.

Haka nan, abu ne mai dadi mutum ya kasance cikin al’umma, wadda ta san martaba da taimakon junanta tare da kai wajen ciyar da al’umma baki-daya gaba.

Sannan, a duk wurin da masu ilimi ke da rinjaye, suna kokarin taimaka wa masu karamin karfi, musamman ta bangarorin da suka gaza, don su ma su samu farin ciki da walwala a tasu rayuwar.

7- Samar Da Al’umma Mai Tafiya Daidai Da Zamani 

Ilimi shi ne babban jagoran ci gaban al’umma, don haka ya kamata mutum ya yi kokari ya san abubuwan da suka shafi al’adunsa, tarihi da kuma sauran al’amuran da suka shafe shi kai tsaye.

Haka zalika, a koda-yaushe ilimi na tafiya ne da zamani; shi yasa masu ilimi ba a taba barin su a baya, wajen rungumar sabbin abubuwan da zamani ke dauke da su.

Har ila yau, kamar yadda kowa ya sani ne cewa, ilimi haske ne; sannan kuma wata kofa ce ta fahimtar dukkanin wasu al’amuran rayuwa.

8- Mu’amala Daban-daban

Ilimin fasahar zamani, na taimakawa wajen hada mutane da kamfanoni daga ko’ina a fadin duniya ba tare da wata katanga ba, muddin dai za a iya yin mu’amala tare da yin musayar ra’ayi da mutane daga wasu kasashe masu al’adu mabambanta, wannan kai tsaye yana nuni ne da irin muhimmancin da ilimi yake da shi.

Sa’annan, ilimi yana matukar taimaka mana wajen sanin juna da yin mu’amala ta kai tsaye, duk kuwa da irin banbance-banbancen da ke tsakaninmu.

9- Samar Da Damar Taimakawa 

Gudunmawar da ilimi ke bayarwa a tsakanin al’umma, na da matukar yawa; duba da cewa, a irin wannan zamani babu wani abu da zai iya yiwuwa ba tare da ilimi ba.

Idan muka dubi bangaren shugabanci, sanin kowa; babu yadda za a yi jahili ya jagoranci al’umma, koda kuwa a Karkara ne; ballantana kuma a Birane.

Haka nan, batun kasuwanci a halin yanzu; musamman yadda duniya ta canja, kusan komai ya zama na ilimi. Don haka, da zarar ka kasance a matsayin jahili; akwai kasuwanci da dama da zai fi karfinka, sai dai ka zama dan kallo.

10- Daga Darajar Dan’adam

Ko shakka babu, babu abin da ke mayar da Dan’adam ya zama cikakken mutum; tamkar Ilimi, domin kuwa wani mabudi ne wanda ke mayar da mara karfi ya zama mai karfi, wanda ba dan kowa ba; ya zama ya gagara a tsakanin al’umma, sakamakon wannan ilimi da yake da shi.

Har ila yau, ilimi ne kadai zai mayar da dan talaka ya zama wani mashahurin malami ko mai mulki ko kuma wani mai fada a ji.

Hakan ya sha faruwa a tsakanin al’umma, domin kuwa ana samun shugaban kasa, gwamna, sanata, minista da sauran makamantansu, wanda dan talakawa ne kowa ya sani; amma darajar ilimi ta ba shi wannan daukaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiMakarantaSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Next Post

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

3 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

4 days ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

6 days ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

3 weeks ago
Next Post
Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

September 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.