• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Ilimi

A kowane lokaci, ilimi na samun tagomashi da kuma girmamawa daga wurin al’umma. Masu ilimi, su ne ke samun ingantacciyar rayuwa, wadda kowa da kowa ke sha’awa ko mararin samun irin ta.

Idan mutane suka karanci bangaren fannonin da ake ribibin su wajen daukar ma’aikata, ko shakka babu suna samun albashi mai matukar tsoka, ta yadda za su taimaki kansu da iyayensu da sauran danginsu baki-daya.

  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma
  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano

Har ila yau, ilimi na sa a samu daukaka; wadda ba a taba zato ba, sannan yana taimakawa wajen cimma kowane irin buri na rayuwa.

Bugu da kari, ilimi na bayar da dama wajen samun kudaden da za su taimaka wa mutum a rayuwarsa ta yau da kullum tare kuma da samun farin ciki ta fuskoki daban-daban.

6- Masu Ilimi Na Matukar Taimaka Wa Al’umma 

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ta wace hanya masu ilimi ke taimaka wa al’umma? Kasancewar masu ilimi, sun san muhimmancinsa tare kuma da sanin abin da ya kamata, shi yasa a duk inda suka fi yawa ake samun zaman lafiya da hadin kai da kuma rayuwa mai inganci.

Haka nan, abu ne mai dadi mutum ya kasance cikin al’umma, wadda ta san martaba da taimakon junanta tare da kai wajen ciyar da al’umma baki-daya gaba.

Sannan, a duk wurin da masu ilimi ke da rinjaye, suna kokarin taimaka wa masu karamin karfi, musamman ta bangarorin da suka gaza, don su ma su samu farin ciki da walwala a tasu rayuwar.

7- Samar Da Al’umma Mai Tafiya Daidai Da Zamani 

Ilimi shi ne babban jagoran ci gaban al’umma, don haka ya kamata mutum ya yi kokari ya san abubuwan da suka shafi al’adunsa, tarihi da kuma sauran al’amuran da suka shafe shi kai tsaye.

Haka zalika, a koda-yaushe ilimi na tafiya ne da zamani; shi yasa masu ilimi ba a taba barin su a baya, wajen rungumar sabbin abubuwan da zamani ke dauke da su.

Har ila yau, kamar yadda kowa ya sani ne cewa, ilimi haske ne; sannan kuma wata kofa ce ta fahimtar dukkanin wasu al’amuran rayuwa.

8- Mu’amala Daban-daban

Ilimin fasahar zamani, na taimakawa wajen hada mutane da kamfanoni daga ko’ina a fadin duniya ba tare da wata katanga ba, muddin dai za a iya yin mu’amala tare da yin musayar ra’ayi da mutane daga wasu kasashe masu al’adu mabambanta, wannan kai tsaye yana nuni ne da irin muhimmancin da ilimi yake da shi.

Sa’annan, ilimi yana matukar taimaka mana wajen sanin juna da yin mu’amala ta kai tsaye, duk kuwa da irin banbance-banbancen da ke tsakaninmu.

9- Samar Da Damar Taimakawa 

Gudunmawar da ilimi ke bayarwa a tsakanin al’umma, na da matukar yawa; duba da cewa, a irin wannan zamani babu wani abu da zai iya yiwuwa ba tare da ilimi ba.

Idan muka dubi bangaren shugabanci, sanin kowa; babu yadda za a yi jahili ya jagoranci al’umma, koda kuwa a Karkara ne; ballantana kuma a Birane.

Haka nan, batun kasuwanci a halin yanzu; musamman yadda duniya ta canja, kusan komai ya zama na ilimi. Don haka, da zarar ka kasance a matsayin jahili; akwai kasuwanci da dama da zai fi karfinka, sai dai ka zama dan kallo.

10- Daga Darajar Dan’adam

Ko shakka babu, babu abin da ke mayar da Dan’adam ya zama cikakken mutum; tamkar Ilimi, domin kuwa wani mabudi ne wanda ke mayar da mara karfi ya zama mai karfi, wanda ba dan kowa ba; ya zama ya gagara a tsakanin al’umma, sakamakon wannan ilimi da yake da shi.

Har ila yau, ilimi ne kadai zai mayar da dan talaka ya zama wani mashahurin malami ko mai mulki ko kuma wani mai fada a ji.

Hakan ya sha faruwa a tsakanin al’umma, domin kuwa ana samun shugaban kasa, gwamna, sanata, minista da sauran makamantansu, wanda dan talakawa ne kowa ya sani; amma darajar ilimi ta ba shi wannan daukaka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.