ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

A kowane lokaci, ilimi na samun tagomashi da kuma girmamawa daga wurin al’umma. Masu ilimi, su ne ke samun ingantacciyar rayuwa, wadda kowa da kowa ke sha’awa ko mararin samun irin ta.

Idan mutane suka karanci bangaren fannonin da ake ribibin su wajen daukar ma’aikata, ko shakka babu suna samun albashi mai matukar tsoka, ta yadda za su taimaki kansu da iyayensu da sauran danginsu baki-daya.

  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma
  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano

Har ila yau, ilimi na sa a samu daukaka; wadda ba a taba zato ba, sannan yana taimakawa wajen cimma kowane irin buri na rayuwa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, ilimi na bayar da dama wajen samun kudaden da za su taimaka wa mutum a rayuwarsa ta yau da kullum tare kuma da samun farin ciki ta fuskoki daban-daban.

6- Masu Ilimi Na Matukar Taimaka Wa Al’umma 

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Ta wace hanya masu ilimi ke taimaka wa al’umma? Kasancewar masu ilimi, sun san muhimmancinsa tare kuma da sanin abin da ya kamata, shi yasa a duk inda suka fi yawa ake samun zaman lafiya da hadin kai da kuma rayuwa mai inganci.

Haka nan, abu ne mai dadi mutum ya kasance cikin al’umma, wadda ta san martaba da taimakon junanta tare da kai wajen ciyar da al’umma baki-daya gaba.

Sannan, a duk wurin da masu ilimi ke da rinjaye, suna kokarin taimaka wa masu karamin karfi, musamman ta bangarorin da suka gaza, don su ma su samu farin ciki da walwala a tasu rayuwar.

7- Samar Da Al’umma Mai Tafiya Daidai Da Zamani 

Ilimi shi ne babban jagoran ci gaban al’umma, don haka ya kamata mutum ya yi kokari ya san abubuwan da suka shafi al’adunsa, tarihi da kuma sauran al’amuran da suka shafe shi kai tsaye.

Haka zalika, a koda-yaushe ilimi na tafiya ne da zamani; shi yasa masu ilimi ba a taba barin su a baya, wajen rungumar sabbin abubuwan da zamani ke dauke da su.

Har ila yau, kamar yadda kowa ya sani ne cewa, ilimi haske ne; sannan kuma wata kofa ce ta fahimtar dukkanin wasu al’amuran rayuwa.

8- Mu’amala Daban-daban

Ilimin fasahar zamani, na taimakawa wajen hada mutane da kamfanoni daga ko’ina a fadin duniya ba tare da wata katanga ba, muddin dai za a iya yin mu’amala tare da yin musayar ra’ayi da mutane daga wasu kasashe masu al’adu mabambanta, wannan kai tsaye yana nuni ne da irin muhimmancin da ilimi yake da shi.

Sa’annan, ilimi yana matukar taimaka mana wajen sanin juna da yin mu’amala ta kai tsaye, duk kuwa da irin banbance-banbancen da ke tsakaninmu.

9- Samar Da Damar Taimakawa 

Gudunmawar da ilimi ke bayarwa a tsakanin al’umma, na da matukar yawa; duba da cewa, a irin wannan zamani babu wani abu da zai iya yiwuwa ba tare da ilimi ba.

Idan muka dubi bangaren shugabanci, sanin kowa; babu yadda za a yi jahili ya jagoranci al’umma, koda kuwa a Karkara ne; ballantana kuma a Birane.

Haka nan, batun kasuwanci a halin yanzu; musamman yadda duniya ta canja, kusan komai ya zama na ilimi. Don haka, da zarar ka kasance a matsayin jahili; akwai kasuwanci da dama da zai fi karfinka, sai dai ka zama dan kallo.

10- Daga Darajar Dan’adam

Ko shakka babu, babu abin da ke mayar da Dan’adam ya zama cikakken mutum; tamkar Ilimi, domin kuwa wani mabudi ne wanda ke mayar da mara karfi ya zama mai karfi, wanda ba dan kowa ba; ya zama ya gagara a tsakanin al’umma, sakamakon wannan ilimi da yake da shi.

Har ila yau, ilimi ne kadai zai mayar da dan talaka ya zama wani mashahurin malami ko mai mulki ko kuma wani mai fada a ji.

Hakan ya sha faruwa a tsakanin al’umma, domin kuwa ana samun shugaban kasa, gwamna, sanata, minista da sauran makamantansu, wanda dan talakawa ne kowa ya sani; amma darajar ilimi ta ba shi wannan daukaka.

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.