• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 16 ga watan nan da muke ciki, rana ce ta tabbatar da wadatar abinci a duniya. Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da wannan batu, da ya zama abin da gwamnatocin kasa da kasa suke mai da hankali kansa a ko da yaushe? Bari mu tantance kokarin da Sin ta yi a wannan bangare, da gudunmawar da take bayarwa duniya.

 

A shekarar 1949, lokacin da aka kafa jamhuriyar jama’ar kasar Sin, yawan hatsin da Sin ta samu shekara daya bai wuce ton miliyan 113.2 ba. Amma a shekarar 2023, wannan adadin ya kai ton miliyan 695, kuma an tabbatar da samun yawan hatsin da ya kai kimanin ton miliyan 650 a cikin shekaru 9 a jere, lamarin da ya sanya Sin samun yabanya mai yalwa cikin shekaru 20 a jere. Kana matsakacin yawan hatsin da kowane Basine ya samu a duk shekara ya kai kilo 493, adadin da ya zarce kilo 400, wanda ya zama ma’aunin duniya na samun wadatar abinci ga ko wane mutum. Abun da ya bayyana cewa, Sinawa na samun wadatar abinci bisa jagorantar da gwamnatinsu ta yi, gami da kokarinsu.

  • Yawan Karuwar GDPn Sin Daga Watan Janairu Zuwa Satumban Bana Ya Kai 4.8% Bisa Na Makamancin Lokacin A Bara
  • Li Qiang Ya Halarci Taron Majalisar Shugabannin Gwamnatocin Kasashe Mambobin SCO Karo Na 23

Mene ne dalilin da ya sa aka samu wannan nasara? Shi ne domin tsarin kare gonaki na kasar, da yadda take yayata fasahar aikin gona. Ya zuwa karshen shekarar 2023, yawan ingantattun gonakin da Sin ta mallaka ya kai fiye da muraba’in kilomita dubu 667. Kuma ba tabbatar da yawansu kadai kasar Sin take yi ba, tana dukufa kan tabbatar da ingancinsu. Kazalika, yawan gudunmawa ta fuskar kimiyya da fasaha da aka samar a bangaren aikin gona a shekarar 2023 ya kai kashi 63.2%, adadin da ya karu da kashi 8.7% bisa na shekarar 2012, matakin da ya sa Sin zama daya daga cikin kasashe mafiya karfin kimiyya da fasahar aikin gona. Sabbin nau’o’in kimiyya da fasaha da Sin take bayarwa, na taimakon kokarin tabbatar da wadatar abinci.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Ban da wannan kuma, hanyar da Sin take bi na tabbatar da wadatar abinci, ya zama abun koyi ga kasashe daban daban, kuma Sin tana hadin gwiwa da sauran kasashe wajen yada fasahohinta. Alali misali, kasar Madagascar, ta rungumi fasahar noman shinkafar da aka tagwaita ta Sin, inda yawan shinkafar da ake nomanta a Madagascar ya kai kadada dubu 70, kana yawan hatsin da ake girba kan kadada daya ya kai ton 7, wani lokaci har ya kan kai ton 12, adadin da ya ninka har sau 2 bisa na nau’in shinkafar asali da ake nomansu a kasar. Ta la’akari da bukatun da ke akwai a kasar Madagascar a duk shekara, za a samu damar tabbatar da wadatar abinci a kasar, idan aka kara shuka irin shinkafar Sin a gonaki masu fadin kadada dubu 100. Domin tunawa da taimakon da Sin ta ba kasar a bangaren shuka shinkafar da aka tagwaita, Madagascar ta buga hoton shinkafar Sin a kan takardar kudinta.

 

Sin ta taka rawar gani wajen tabbatar da wadatar abinci. Kuma tana kokarin gabatar da dabarunta ga sauran kasashe. Shi ya sa, karin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afrika, ke da damar tabbatar da wadatar abinci, ta hanyar amfani da fasahar Sin. Sinawa su kan ce “More tare da sauran mutane ya fi jin dadin wani abu mutum daya kadai ”. Sin na son raba dabararta ta hanyar hadin gwiwa da sauran kasashe a dukkan fannoni. (MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Ne Ke Tallafa Wa Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Da Kudade?

Next Post

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

2 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

3 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

4 hours ago
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

5 hours ago
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

6 hours ago
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

7 hours ago
Next Post
Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.