• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

by Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan yakin ciniki ya kasance guguwar da Amurka ta tayar a duniya, to hakan zai sa Sin da Afirka su kara rike hannayen juna.

A yau, an gudanar da taron ministocin masu kula da yadda ake aiwatar da sakamakon da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, a birnin Changsha na kasar Sin. A wajen taron, an gabatar da sanarwar ta Changsha game da hadin gwiwar Sin da Afirka a kokarin tabbatar da hadin kan kasashe masu tasowa.

  • Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
  • Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

Za a iya cewa, sanarwar hadin gwiwa ce da Sin da Afirka suka fitar a madadin daukacin kasashe masu tasowa, domin nuna kin amincewa da ra’ayin kashin kai, da yadda ake kashin dankali a duniya. A cikin wannan sanarwa, Sin da Afirka sun yi nuni da cewa, “rikicin da ake fama da shi a duniya, na samun ra’ayin kashin kai, da na kariyar ciniki, da cin zarafin wasu kasashe a fannin tattalin arziki, ya haddasa babbar matsala ga dimbin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka”, tare da yin kira ga dukkan kasashe, musamman Amurka, da su koma kan turbar da ta dace ta yin shawarwari, da musayar ra’ayi kan sabanin ra’ayi a fannin ciniki.

Wannan sanarwar ta kunshi tofin Allah tsine ga yakin harajin fito, da yakin ciniki da Amurka ta kaddamar. Saboda kasar Sin da kasashen dake nahiyar Afirka da dama sun samu ‘yancin kai ne bisa yaki da ‘yan mulkin mallaka, da na mulkin danniya. Saboda haka tarihin gwagwarmaya ya ba su kwarin gwiwar tabbatar da adalci da kare mutunci. Ban da wannan kuma, a yayin da ake fuskantar cin zarafi na tattalin arziki da Amurka ke yi, Sin da Afirka ma suna da kwarin gwiwar hada karfi da karfe don samun nasara a fafutukar da suke ta kare moriyarsu.

Wannan kwarin gwiwa, da farko ya fito ne daga yadda kasar Sin ta mayar da martani ga yakin ciniki da kasar Amurka ta kaddamar. Bayan da kasar Sin ta samu tsokanar harajin kwastam mafi tsanani da Amurka ta saka mata, kasar Sin ba ta tsoro, kuma ba ta ja da baya ba, maimakon haka ta yi amfani da tsauraran matakan karbar karin haraji fito kan Amurka, da na hana fitar da wasu ma’adinai masu muhimmanci, don tilastawa Amurka komawa teburin tattaunawa. Ta haka, an baiwa duniya damar fahimtar halayyar “mai zalunci” da ke son nuna karfin tuwo, amma a hakika shi ma zai ji tsoro, idan a nuna masa karfi, da kwarin gwiwar da ake da shi.

Labarai Masu Nasaba

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

Don haka, a cikin sanarwar da aka fitar a wannan karo, kasashen Afirka sun nuna yabo kan jajircewar kasar Sin, da kuma kudurin da kasar ta dauka na kare adalci, da kuma ingancin tsare-tsaren tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa. Har ila yau, kasar Sin ita ma ta nuna godiya ga kasashen Afirka, kan yadda suke bin ka’idojin kare ‘yancin kai, da adalci, tare da tsayawa kan matsaya guda wajen fuskantar matsin lamba da aka sanya musu.

Hakika idan mun tantance kwarin gwiwar Sin da Afirka, za mu ga da farko ya zo daga dangantakarsu mai dorewa ta hadin gwiwa da juna. Za mu iya daukar misalin bangaren ciniki: daga shekarar 2000, lokacin da aka kafa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, zuwa bara, yawan ciniki tsakanin Sin da Afirka ya karu daga dalar Amurka biliyan 13.92 zuwa dalar Amurka biliyan 295.56, wanda ya karu da fiye da sau 20. Kana kasar Sin ta kasance abokiyar ciniki ta Afirka mafi girma a duniya tsawon shekaru 16 a jere. Sa’an nan, a watanni hudu na farkon bana, darajar ciniki tsakanin Sin da Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 103.1, adadin da ya karu da kashi 8.1% bisa na makamancin lokacin bara. Kana idan mun duba nan gaba, a cikin wasikar taya murna ga taron da aka gudanar a birnin Changsha, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, za a aiwatar da shirin ba da damar yafe harajin fito 100% ga kasashe 53 dake nahiyar Afirka masu huldar diflomasiyya da kasar Sin, kana a sa’i daya kuma, zai samar da karin sauki ga kasashe mafin karancin tattalin arziki a Afirka don su fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin. Wadannan alkaluman da na ambata sun nuna cewa, daga a baya har zuwa yau, da kuma nan gaba, hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka na kara habaka. Wannan ya nuna yadda amintattun abokan hadin gwiwa ya kamata su kasance tare da juna.

Ko ta yaya wasu kasashe ke tayar da hankali a duniya, za mu iya ganin wannan hoto: Sin da Afirka, aminai na kwarai, suna tsayawa tare da juna, rike da hannayen juna, a kokarin tabbatar da ci gaban kasashensu na bai daya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Faretin Ranar Dimokuraɗiyya, Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Ƙasa Jawabi 

Next Post

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

Related

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

24 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

2 days ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 week ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

1 week ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Next Post
Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

LABARAI MASU NASABA

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

July 4, 2025
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

July 4, 2025
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

July 4, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

July 4, 2025
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

July 4, 2025
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.