• English
  • Business News
Thursday, June 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

by Sulaiman
1 day ago
in Ra'ayi Riga
0
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan yakin ciniki ya kasance guguwar da Amurka ta tayar a duniya, to hakan zai sa Sin da Afirka su kara rike hannayen juna.

A yau, an gudanar da taron ministocin masu kula da yadda ake aiwatar da sakamakon da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, a birnin Changsha na kasar Sin. A wajen taron, an gabatar da sanarwar ta Changsha game da hadin gwiwar Sin da Afirka a kokarin tabbatar da hadin kan kasashe masu tasowa.

  • Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
  • Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

Za a iya cewa, sanarwar hadin gwiwa ce da Sin da Afirka suka fitar a madadin daukacin kasashe masu tasowa, domin nuna kin amincewa da ra’ayin kashin kai, da yadda ake kashin dankali a duniya. A cikin wannan sanarwa, Sin da Afirka sun yi nuni da cewa, “rikicin da ake fama da shi a duniya, na samun ra’ayin kashin kai, da na kariyar ciniki, da cin zarafin wasu kasashe a fannin tattalin arziki, ya haddasa babbar matsala ga dimbin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka”, tare da yin kira ga dukkan kasashe, musamman Amurka, da su koma kan turbar da ta dace ta yin shawarwari, da musayar ra’ayi kan sabanin ra’ayi a fannin ciniki.

Wannan sanarwar ta kunshi tofin Allah tsine ga yakin harajin fito, da yakin ciniki da Amurka ta kaddamar. Saboda kasar Sin da kasashen dake nahiyar Afirka da dama sun samu ‘yancin kai ne bisa yaki da ‘yan mulkin mallaka, da na mulkin danniya. Saboda haka tarihin gwagwarmaya ya ba su kwarin gwiwar tabbatar da adalci da kare mutunci. Ban da wannan kuma, a yayin da ake fuskantar cin zarafi na tattalin arziki da Amurka ke yi, Sin da Afirka ma suna da kwarin gwiwar hada karfi da karfe don samun nasara a fafutukar da suke ta kare moriyarsu.

Wannan kwarin gwiwa, da farko ya fito ne daga yadda kasar Sin ta mayar da martani ga yakin ciniki da kasar Amurka ta kaddamar. Bayan da kasar Sin ta samu tsokanar harajin kwastam mafi tsanani da Amurka ta saka mata, kasar Sin ba ta tsoro, kuma ba ta ja da baya ba, maimakon haka ta yi amfani da tsauraran matakan karbar karin haraji fito kan Amurka, da na hana fitar da wasu ma’adinai masu muhimmanci, don tilastawa Amurka komawa teburin tattaunawa. Ta haka, an baiwa duniya damar fahimtar halayyar “mai zalunci” da ke son nuna karfin tuwo, amma a hakika shi ma zai ji tsoro, idan a nuna masa karfi, da kwarin gwiwar da ake da shi.

Labarai Masu Nasaba

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Don haka, a cikin sanarwar da aka fitar a wannan karo, kasashen Afirka sun nuna yabo kan jajircewar kasar Sin, da kuma kudurin da kasar ta dauka na kare adalci, da kuma ingancin tsare-tsaren tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa. Har ila yau, kasar Sin ita ma ta nuna godiya ga kasashen Afirka, kan yadda suke bin ka’idojin kare ‘yancin kai, da adalci, tare da tsayawa kan matsaya guda wajen fuskantar matsin lamba da aka sanya musu.

Hakika idan mun tantance kwarin gwiwar Sin da Afirka, za mu ga da farko ya zo daga dangantakarsu mai dorewa ta hadin gwiwa da juna. Za mu iya daukar misalin bangaren ciniki: daga shekarar 2000, lokacin da aka kafa dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, zuwa bara, yawan ciniki tsakanin Sin da Afirka ya karu daga dalar Amurka biliyan 13.92 zuwa dalar Amurka biliyan 295.56, wanda ya karu da fiye da sau 20. Kana kasar Sin ta kasance abokiyar ciniki ta Afirka mafi girma a duniya tsawon shekaru 16 a jere. Sa’an nan, a watanni hudu na farkon bana, darajar ciniki tsakanin Sin da Afirka ta kai dalar Amurka biliyan 103.1, adadin da ya karu da kashi 8.1% bisa na makamancin lokacin bara. Kana idan mun duba nan gaba, a cikin wasikar taya murna ga taron da aka gudanar a birnin Changsha, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana cewa, za a aiwatar da shirin ba da damar yafe harajin fito 100% ga kasashe 53 dake nahiyar Afirka masu huldar diflomasiyya da kasar Sin, kana a sa’i daya kuma, zai samar da karin sauki ga kasashe mafin karancin tattalin arziki a Afirka don su fitar da kayayyaki zuwa kasar Sin. Wadannan alkaluman da na ambata sun nuna cewa, daga a baya har zuwa yau, da kuma nan gaba, hadin gwiwar cinikayya tsakanin Sin da Afirka na kara habaka. Wannan ya nuna yadda amintattun abokan hadin gwiwa ya kamata su kasance tare da juna.

Ko ta yaya wasu kasashe ke tayar da hankali a duniya, za mu iya ganin wannan hoto: Sin da Afirka, aminai na kwarai, suna tsayawa tare da juna, rike da hannayen juna, a kokarin tabbatar da ci gaban kasashensu na bai daya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Faretin Ranar Dimokuraɗiyya, Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Ƙasa Jawabi 

Next Post

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

Related

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

2 days ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 days ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

1 week ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

1 week ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

2 weeks ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

3 weeks ago
Next Post
Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

LABARAI MASU NASABA

Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

June 12, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

June 12, 2025
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

June 12, 2025
Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

June 12, 2025
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

June 12, 2025
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha

June 12, 2025
Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote

June 12, 2025
Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara

June 12, 2025
Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

Ya Kamata Ana Kammala Shari’ar Zaɓe Kafin Rantsuwa

June 12, 2025
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.