• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 weeks ago
Kwastam

Guguwar ritaya mai karfi za ta girgiza Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) a shekarar 2026, yayin da jami’ai 825 za su bar aiki bisa ka’idar ritaya, kamar yadda jaridar LEADERSHIP Hausa ta gano.

 

A watan Agusta na shekarar 2025 rahotanni sun bayyana cewa akalla jami’ai 791 na hukumar za su yi ritaya a shekarar 2026, Sai dai kamar yadda aka zata, adadin ya karu zuwa 825, karin mutum 34, bisa jerin sunayen da hukumar ta sanya suna: “Jerin karshe Na Jami’ai Da Ma’aikata Don Ritaya A Shekarar 2026.

  • Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
  • Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Wannan adadi ya zama babba idan aka kwatanta da yawan ma’aikatan hukumar gaba daya da ke kusan 18,000 a fadin kasar nan wanda ya yi kasa sosai da 30,000 da Majalisar Tarayya ta tsara a matsayin adadin da hukumar ke bukata.

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Wannan lamari ya haifar da tambaya kan yiwuwar dorewar shirin sauye-sauye da na zamani da ake gudanarwa a karkashin jagorancin Babban Kwanturola Janar, Adewale Adeniyi.

 

Adewale Adeniyi, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kara wa wa’adin mulki na shekara guda, shima zai yi ritaya daga hukumar a watan Agusta, 2026.

 

A halin yanzu, za a dauki babban mataki kafin a cike gibin ma’aikata da ake bukata a hukumar kwastam, musamman idan aka yi la’akari da cewa jami’ai 825 za su bar aiki ba tare da sabon daukar ma’aikata ba.

 

Binciken da leadership Hausa ta gudanar ya gano cewa ritayar ta shafi kowane mataki a hukumar daga manyan shugabanni, zuwa matsakaita, har da kananan jami’ai.

 

Daga cikin jami’ai 825 da za su yi ritaya saboda shekaru 60 da suka kai ko kuma shekaru 35 na aiki:

 

5 suna da mukamin mataimakan kwanturola na kasa wato (DCG) sai wasu kananan mataimaka Kwanturola na kasa (ACG) su 13 sai kuma Kwanturololi ( CAC) guda 53 da mataimakanau (DC) guda 51 kananan mataimaka Kwanturola ( AC) guda 46.

 

Sauran sune ; masu mukaman (CSC) guda 61 sai ( SC) Guda 226 da ( DSC) su 285 sai (ASC I) 64 da (ASC II) su 10 (IC), su 8 (CA I) guda 1 sai (CA II) su 2 Jami’an mataimaka Kwanturola Janar ( DCG) guda biyar da ritayar ta shafa su ne: Mista C.K. Niagwan da K.I. Adeola da kuma Mista S. Chiroma; Mr. G.M. Omale; da Mista A. Nnadi.

 

Kananan Jami’an mataimaka Kwanturola Janar (ACG) guda goma sha uku (13) da abin ya shafa su ne: K.C. Egwuh, M.S. Yusuf, da Z.M. Gaji da N.P. Umoh da O.A. Adebakin da kuma T. Bomodi da B.O. Olomu, O.P. Olaniyan, I.K. Oladeji, K. Mohammed, O.A. Adebakin, da B. Mohammed, da C.C. Dim.

 

Daga cikin Kwanturololi da za su yi ritaya a 2026, akwai: D. Abubakar, da O.Y. Shuaibu, F.A. Bodunde da P.C. Chibuoke, da kuma O.O. Akingbade, da A. Salihu, da wasu da dama.

 

A matsayin shiri kafin ranar ritayar 2026, Hedikwatar Hukumar Kwastam da ke Abuja ta bayar da umarni ga dukkan jami’an da abin ya shafa su fara shirye-shiryen barin aiki kamin ranar ta isko su.

 

Hakazalika, An umurce su da su mika sanarwar izinin hutu na watanni uku kafin ritaya ga Babban Kwanturola Janar na Kwastam (CGC).

 

A cikin takardar da wakilinmu ya gani mai taken “Jerin karshe Na Jami’ai da Ma’aikata Don Ritaya A Shekarar 2026”, wacce aka fitar ranar 19 ga Satumba, 2025, kuma Kwanturola A.A. Bazuaye ya sanya hannu a madadin DCG na Sashen Albarkatun Dan Adam (HR), an bukaci jami’an da abin ya shafa da su bi doka da tsari.

 

Kamar yadda takardar ta ce: “A bisa Dokar Aikin Gwamnati (PSR No. 100238) da kuma Sanarwar Gwamnati mai lamba 36216/S.1/D/T: CR1/2001/5 na 20/3/2001, dukkan jami’an da suka cika shekarun ritaya a 2026 za su bar aiki kuma su tafi hutu na watanni uku kafin ranar da ritayar za ta fara aiki.”

 

Haka kuma, an umurci dukkan jami’an da abin ya shafa su tabbatar da bin umarnin, tare da tura takardar sanarwar hutun ritayarsu ga Babban Kwanturola Janar yadda ya dace.

 

Takardar ta kuma bukaci Koordinetocin Yankuna da Kwamandojin Yankuna su sanar da duk jami’an da abin ya shafa a yankunansu.

 

Da wannan yawan ma’aikata da za su bar aiki a 2026, har yanzu ana cikin tunanin irin dabarar da shugabancin kwastam zai yi amfani da ita don cike gibin da zai biyo baya, tare da tabbatar da ci gaba da sabbin domin gudanar da ayyukan hukumar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari'a Da Inganta Shugabanci A Duniya

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.