• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwagwarmayar Kwato Wa Ma’aikata Hakkinsu A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwagwarmayar Kwato Wa Ma’aikata Hakkinsu A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da Nijeriya ta shiga sahun sauran kasashen duniya wajen bikin ranar ma’aikata ta duniya, yana da matukar muhimmanci mu yi nazari a kan hakki da gwagwamaryar ma’aikata a Nijeriya zuwa yanzu. Ranar ba wai ana nufin kawai a bayar da hutu ba ce a kuma yi fareti da bukukuwa kawai ba ne, ranar ce ta duba gudummawar ma’aikata da sadaukarwar da suka yi wajen gina kasa kuma gashi suna ci gaba da bayar da gudummawar ganin kasa ta samu ci gaban  da ake bukata.

Ya kamata al’umma su fahimmaci cewa, ranar ma’aikata ko kuma kamar yadda wasu ke kiranta da suna ‘May Day’ ya samo asali ne daga kungiyoyin gwagwarmayar nema wa ma’aikata hakkokinsu. Ranar ta samo asali ne daga kasar Amurka a karni na 19 tun daga wancan  lokaci kuma ake bukukuwan ranar a fadin duniya gaba daya.

  • Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa
  • Wasu Ke Neman Bata Mana Suna Kan Rikicin Shugabancin APGA – INEC

A Nijeriya an fara bikin ranar ne a shekarar 1980, bayan da gwamnatin soja ta Janar Olusegun Obasanjo ta ayyana ranar a matsayin ranar hutu.

A tsawon shekaru, ma’aikatan Nijeriya sun yi gwagwamarya daban-daban ta neman hakkokinsu wadanda suka hada da hakkin kafa kungiya da hakkin nemawa kansu hakkokinsu a kungiyance, da hakkin kariya daga cuttutuka a wajen aiki da bukatar a samar masu da mafi karancin albashi don su samu gudanar da aiki a cikin kwanciyar hankali.

Amma kuma a ra’ayin wannan jaridar har zuwa yanzu ba dukkan ma’aikatan Nijeriya ke amfana da wadannan hakkokin ba, da yawa daga cikin ma’aikatan Nieriya na ci gaba ne da fuskantar matsaloli da suka hada da rashin albashi mai inganci da kuna yadda ake nuna masu bambanci da kuma yadda suke aiki a cikin yanayi mai cutar da rayuwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Tabbas batun mafi karancin albashi shi ne lamari mafi girma a cikin matsalolin da ma’aikata suke fuskanta a Nijeriya. Jihoji da dama sun kasa biyan albashin ma’aikata. Wani rahoto na wata kungiya mai zaman kanta mai suna BudgIT, ta bayyana cewa a shekarar da ta wuce akawai jihohi 12 daga cikn jihohi 36 da muke da su na kasa akalla sun kasa biyan ma’aikata albashin daya ko biyu, wasu jihohin ma bashin da ma’aikata ke bin su na albashi da ya wuce na wata 6 wasu na bin bashin albashin fiye da shekara 3.

Wannan kuma yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu gwamnanoni ke kaddamar da wasu manyan ayyukan da babu yadda za a iya yinsu suna kuma zartar da kasafin manyan kudaden da za a rinka biyansu bayan in sun yi ritaya, ba za mu amince da wannan lamarin ba.

Gwamnatin tarayya na shirin cire tallafin man fetur wanda hakan kuma zai kara tsawalla tsadar kayan masarufi da harkokin rayuwar yau da kullun ta al’umma, a kan haka ne ya dace, gwamnati mai jiran kama madafun iko ta Bola Hamed Tinubu ta kara wa ma’aikata albashi tare da sauran abubuwan da za su rage radadin da za a shiga sakamakon cire tallafin man.

Wannan jaridar ta nuna kyamarta a kan yadda kungiyoyin ma’aikata ke shiga yajin aiki daga an samu wata takaddama, muna kuma godiya ga gwmanatin tarayya a kan yadda ta fara cika wa ma’aikatan alkawurransu, a ra’ayinmu, rajin aiki ya zama wani tsohon yayi, ya kuma kamata gwamnatin tarayya ta tabbatar da tana cikia dukkan alkawarin da ta dauka a tsakaninta da kungiyoyin kwadago a kowane lokaci.

Babu tantamamr cewa, babbar matsalar da ma’aikatan Nijeriya ke fuskanta a wannann lokacin ita ce ta rashin tabbas a wurin ayyukansu. Ma’aikata da dama a bangaren kamfanoni masu zaman kansu ana daukar su ne ba a tsarin dindindin ba, basu da wani tsari na taimaka wa rauyuwar su bayan sun ajiye aiki, kamar tsarin fansho da inshorar lafiya, wanda hakan yana cutar da rayuwarsu bayan sun tsufa sun ajiye aiki.

Wata matsalar da ma’aikata  Nijeriye ke fuskanta ya hada da yadda ake nuna masu bambanci, musamman bambancin da ake nuna wa mata. Mata na cikin kaso mafi yawa na ma’aikatan Nijeriya amma suna fuskantar barazana da tsagwama a wuraren aikinsu.

Duk da wadannan  kalubalen, ma’aikata a Nijeriya na ci gaba da fafutuka neman hakokkinsu ta hanyoyoin kungiyoyin NLC da TUC, sun ci gaba da gwagwarmayar nema wa ma’aikata hakkokinsu da suka hada da albashi mai tsoka da yanayin aiki mai kyau ba tare da takura ba, sun kuma taka rawar gani a kokarin yaki da nuna bambaci a tsakanin mata, ta yadda kowa za iya aiki a cikin walwala ba tare da fargaba ko wata takura ba.

Ya zama dole mu ci gaba da mutumtawa tare da tuna gudummawar da ma’aikata suka bayar a wajen tabbatar da mutuncin ma’aikata a fadin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kwato 'YanciMa'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

NUT Ta Yabawa El-Rufai Kan Dawo Da Korarrun Malaman Makaranta 1,288 Bakin Aiki

Next Post

ISWAP Sun Kashe ‘Yan Gudun Hijira 3 Da Raunata Sojoji 8 Da Wasu 5 A Borno

Related

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

1 hour ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

4 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

18 hours ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

1 day ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

1 day ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

1 day ago
Next Post
Kwamandojin ‘Yan Ta’adda, Ba’a Usman, Alhaji Ari, Da Wasu Da Dama Sun Mika Wuya Ga Sojoji

ISWAP Sun Kashe ‘Yan Gudun Hijira 3 Da Raunata Sojoji 8 Da Wasu 5 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.