• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin gwamnatin Jihar Bauchi na toshe kafofin sata da handame dukiyar al’ummar, ta kirkiro wata hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai suna ‘Bauchi State Public Complaints and Anti-Corruption Commission’ wanda tuni aka sanya mata hannu domin ta fara aiki gadan-gadan.

Da yake sanya hannu kan kudirin dokar bayan da majalisar dokokin jihar ta kammala bitarsa tare da amincewa da shi, gwamna Bala Muhammad, ya ce an samar da kudirin ne domin tabbatar da dakile masu yin zagon kasa ta hanyar cinye dukiyar al’umma daga cikin ma’aikatan gwamnati, ‘yan siyasa da kuma al’umma a fadin jihar.

  • Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a
  • Gidauniyar Masari Ta Tallafa Wa Marasa Karfi A Jihar Katsina

Ya nanata cewar hukumar za ta samu cikakken ‘yancin gudanar da aikinta ba tare da yi mata katsalandan daga gwamnati ba, kana ya kuma tabbatar da cewa ba an kafa hukumar ne domin ta musguna wa abokan adawarsu a siyasa ba ne, illa domin tsarkake jihar daga harkokin cin hanci da amsar rashawa ta fannoni daban-daban.

A cewarsa: “Gwamnatin jihar Bauchi ta kwaikwayi sauran jihohi wadda dokar Nijeriya ta basu dama su fito da ma’aikatun da za su taimaka wajen sarrafa gwamnati da dakile cin hanci da rashawa da sama da fadi da dukiyar al’umma.

“Ba tare da cin mutuncin mutane ba, ba tare da sanya siyasa a ciki ba wajen yaki da rashawa ba.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

“Shi ya sa muma muka je muka duba dokoki har muka yi wannan kudirin dokar tare da tura wa majalisar dokokin jiha domin dubawa da tantancewa.

“Hukumace wacce ta samu asali daga yanayin da Nijeriya take, muna kara yin yawa kuma akwai bukatar hana wadannan munanan al’adu da dabi’u na cin hanci da rashawa a cikin al’umma,” ya fada.

Gwamna Bala, ya nuna cewa hukumar za ta taimaka sosai wajen saurin duba kesa-kesan rashawa lura da cewa hukumomin Gwamnatin tarayya irin su EFCC da ICPC suna nasu kokarin amma samar da wannan hukumar zai taimaka matuka wajen gudanar da kesa-kesai tun daga matakin farko.

Gwamnan ya ce hukumar za ta kasance ne kamar sauran hukumomin yaki da hancin hanci da rashawa wacce za a mata cikakken tsarin gudanarwa da daukan ma’aikatan da suka dace, ya kuma ce za su fara ne da nada manyan jami’an hukumar da za su jagoranci tafiyar ta da ita, “mutane masu gaskiya da adalci za mu nemo. Kuma za mu tabbatar an baiwa hukumar cikakken ‘yanta domin ta gudanar da aikinta a kashin Kai ba tare da ana shiga mata aiki ba. Ba Musguna ma wani ko wasu za a yi ba, amma so muke a tabbatar da gaskiya wajen gudanar da harkokin gwamnati.”

Bala Muhammad ya kuma ce samar da hukumar wani karin nasara ne ga gwamnatinsa. Sai ya jinjina wa Majalisar dokokin Jihar bisa gaggauwa sanya hannu kan dokar bayan da suka fahimci tasirin da za hakan zai yi ga cigaban jihar.

Tun da farko Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Sulaiman, ya ce a watan da ta gabata ne aka aike wa Majalisar kudirin Kuma Nan take suka zauna domin bita da yin abubuwan da suka dace a kai har ta kai ga sun amince da dokar.

Mataimakinsa Danlami Kawule ne ya wakilce shi a wajen sanya hannun, ya ce sun duba alfanu da muhimmanci kudirin ne ya sanya suka amince da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MuhammadBauchiCin Hanci Da RashawaHukuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a

Next Post

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

9 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

12 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

12 hours ago
Bauchi
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

14 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

15 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

16 hours ago
Next Post
Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Bauchi

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.