• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin gwamnatin Jihar Bauchi na toshe kafofin sata da handame dukiyar al’ummar, ta kirkiro wata hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai suna ‘Bauchi State Public Complaints and Anti-Corruption Commission’ wanda tuni aka sanya mata hannu domin ta fara aiki gadan-gadan.

Da yake sanya hannu kan kudirin dokar bayan da majalisar dokokin jihar ta kammala bitarsa tare da amincewa da shi, gwamna Bala Muhammad, ya ce an samar da kudirin ne domin tabbatar da dakile masu yin zagon kasa ta hanyar cinye dukiyar al’umma daga cikin ma’aikatan gwamnati, ‘yan siyasa da kuma al’umma a fadin jihar.

  • Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a
  • Gidauniyar Masari Ta Tallafa Wa Marasa Karfi A Jihar Katsina

Ya nanata cewar hukumar za ta samu cikakken ‘yancin gudanar da aikinta ba tare da yi mata katsalandan daga gwamnati ba, kana ya kuma tabbatar da cewa ba an kafa hukumar ne domin ta musguna wa abokan adawarsu a siyasa ba ne, illa domin tsarkake jihar daga harkokin cin hanci da amsar rashawa ta fannoni daban-daban.

A cewarsa: “Gwamnatin jihar Bauchi ta kwaikwayi sauran jihohi wadda dokar Nijeriya ta basu dama su fito da ma’aikatun da za su taimaka wajen sarrafa gwamnati da dakile cin hanci da rashawa da sama da fadi da dukiyar al’umma.

“Ba tare da cin mutuncin mutane ba, ba tare da sanya siyasa a ciki ba wajen yaki da rashawa ba.”

Labarai Masu Nasaba

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

“Shi ya sa muma muka je muka duba dokoki har muka yi wannan kudirin dokar tare da tura wa majalisar dokokin jiha domin dubawa da tantancewa.

“Hukumace wacce ta samu asali daga yanayin da Nijeriya take, muna kara yin yawa kuma akwai bukatar hana wadannan munanan al’adu da dabi’u na cin hanci da rashawa a cikin al’umma,” ya fada.

Gwamna Bala, ya nuna cewa hukumar za ta taimaka sosai wajen saurin duba kesa-kesan rashawa lura da cewa hukumomin Gwamnatin tarayya irin su EFCC da ICPC suna nasu kokarin amma samar da wannan hukumar zai taimaka matuka wajen gudanar da kesa-kesai tun daga matakin farko.

Gwamnan ya ce hukumar za ta kasance ne kamar sauran hukumomin yaki da hancin hanci da rashawa wacce za a mata cikakken tsarin gudanarwa da daukan ma’aikatan da suka dace, ya kuma ce za su fara ne da nada manyan jami’an hukumar da za su jagoranci tafiyar ta da ita, “mutane masu gaskiya da adalci za mu nemo. Kuma za mu tabbatar an baiwa hukumar cikakken ‘yanta domin ta gudanar da aikinta a kashin Kai ba tare da ana shiga mata aiki ba. Ba Musguna ma wani ko wasu za a yi ba, amma so muke a tabbatar da gaskiya wajen gudanar da harkokin gwamnati.”

Bala Muhammad ya kuma ce samar da hukumar wani karin nasara ne ga gwamnatinsa. Sai ya jinjina wa Majalisar dokokin Jihar bisa gaggauwa sanya hannu kan dokar bayan da suka fahimci tasirin da za hakan zai yi ga cigaban jihar.

Tun da farko Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Sulaiman, ya ce a watan da ta gabata ne aka aike wa Majalisar kudirin Kuma Nan take suka zauna domin bita da yin abubuwan da suka dace a kai har ta kai ga sun amince da dokar.

Mataimakinsa Danlami Kawule ne ya wakilce shi a wajen sanya hannun, ya ce sun duba alfanu da muhimmanci kudirin ne ya sanya suka amince da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MuhammadBauchiCin Hanci Da RashawaHukuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a

Next Post

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa
Labarai

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

4 minutes ago
Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

3 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

6 hours ago
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

8 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

10 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

12 hours ago
Next Post
Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.