• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar

by Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
Gwaman Bauchi Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Yaki Da Rashawa Ta Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin gwamnatin Jihar Bauchi na toshe kafofin sata da handame dukiyar al’ummar, ta kirkiro wata hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai suna ‘Bauchi State Public Complaints and Anti-Corruption Commission’ wanda tuni aka sanya mata hannu domin ta fara aiki gadan-gadan.

Da yake sanya hannu kan kudirin dokar bayan da majalisar dokokin jihar ta kammala bitarsa tare da amincewa da shi, gwamna Bala Muhammad, ya ce an samar da kudirin ne domin tabbatar da dakile masu yin zagon kasa ta hanyar cinye dukiyar al’umma daga cikin ma’aikatan gwamnati, ‘yan siyasa da kuma al’umma a fadin jihar.

  • Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a
  • Gidauniyar Masari Ta Tallafa Wa Marasa Karfi A Jihar Katsina

Ya nanata cewar hukumar za ta samu cikakken ‘yancin gudanar da aikinta ba tare da yi mata katsalandan daga gwamnati ba, kana ya kuma tabbatar da cewa ba an kafa hukumar ne domin ta musguna wa abokan adawarsu a siyasa ba ne, illa domin tsarkake jihar daga harkokin cin hanci da amsar rashawa ta fannoni daban-daban.

A cewarsa: “Gwamnatin jihar Bauchi ta kwaikwayi sauran jihohi wadda dokar Nijeriya ta basu dama su fito da ma’aikatun da za su taimaka wajen sarrafa gwamnati da dakile cin hanci da rashawa da sama da fadi da dukiyar al’umma.

“Ba tare da cin mutuncin mutane ba, ba tare da sanya siyasa a ciki ba wajen yaki da rashawa ba.”

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

“Shi ya sa muma muka je muka duba dokoki har muka yi wannan kudirin dokar tare da tura wa majalisar dokokin jiha domin dubawa da tantancewa.

“Hukumace wacce ta samu asali daga yanayin da Nijeriya take, muna kara yin yawa kuma akwai bukatar hana wadannan munanan al’adu da dabi’u na cin hanci da rashawa a cikin al’umma,” ya fada.

Gwamna Bala, ya nuna cewa hukumar za ta taimaka sosai wajen saurin duba kesa-kesan rashawa lura da cewa hukumomin Gwamnatin tarayya irin su EFCC da ICPC suna nasu kokarin amma samar da wannan hukumar zai taimaka matuka wajen gudanar da kesa-kesai tun daga matakin farko.

Gwamnan ya ce hukumar za ta kasance ne kamar sauran hukumomin yaki da hancin hanci da rashawa wacce za a mata cikakken tsarin gudanarwa da daukan ma’aikatan da suka dace, ya kuma ce za su fara ne da nada manyan jami’an hukumar da za su jagoranci tafiyar ta da ita, “mutane masu gaskiya da adalci za mu nemo. Kuma za mu tabbatar an baiwa hukumar cikakken ‘yanta domin ta gudanar da aikinta a kashin Kai ba tare da ana shiga mata aiki ba. Ba Musguna ma wani ko wasu za a yi ba, amma so muke a tabbatar da gaskiya wajen gudanar da harkokin gwamnati.”

Bala Muhammad ya kuma ce samar da hukumar wani karin nasara ne ga gwamnatinsa. Sai ya jinjina wa Majalisar dokokin Jihar bisa gaggauwa sanya hannu kan dokar bayan da suka fahimci tasirin da za hakan zai yi ga cigaban jihar.

Tun da farko Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Abubakar Sulaiman, ya ce a watan da ta gabata ne aka aike wa Majalisar kudirin Kuma Nan take suka zauna domin bita da yin abubuwan da suka dace a kai har ta kai ga sun amince da dokar.

Mataimakinsa Danlami Kawule ne ya wakilce shi a wajen sanya hannun, ya ce sun duba alfanu da muhimmanci kudirin ne ya sanya suka amince da shi.

Tags: Bala MuhammadBauchiCin Hanci Da RashawaHukuma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa: Ya Dace Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Shinkafa – Dan Sa’a

Next Post

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Related

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga
Rahotonni

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

1 min ago
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu
Labarai

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

12 hours ago
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata
Labarai

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

12 hours ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

15 hours ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

17 hours ago
Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda
Labarai

Yadda Matashi Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 10 Fyade A Bauchi

17 hours ago
Next Post
Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

Jakadiyar Nijeriya A Kongo Ta Tallafa Wa Marasa Galihu 3,000 A Chikun

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

Nijeriya Ce Ta 37 A Kasashen Da Suka Fi Fama Da Ciwon Siga -Kididdiga

June 3, 2023
Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

June 3, 2023
Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

June 2, 2023
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

June 2, 2023
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

June 2, 2023
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

June 2, 2023
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

June 2, 2023
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

June 2, 2023
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

June 2, 2023
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

June 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.