• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Gwamnan Bauchi A Zamanin Mulkin Soja

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Gwamnan Bauchi A Zamanin Mulkin Soja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya nuna matuƙar ƙaduwa da samun labarin rasuwar Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), Sarkin Zuru da ke jihar Kebbi kuma tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a zamanin mulkin soja, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 82 a duniya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya. 

 

Gwamnan ya ce, “Dukkanin abinda muka samu daga Allah ne, haka ma wanda muka rasa, sai dai mu miƙa komai gare shi domin samun dacewa. Mun wayi gari da rasuwar shugaba, uba, jagora kuma abin koyi, tsohon gwamnan jiharmu ta Bauchi a mulkin soji, kuma mai martaba Sarkin Zuru, Manjo Janar Sani Sami (rtd).”

  • Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
  • Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Gwamnan ya ƙara da cewa (Baba) Sami ya mulki jihar Bauchi daga 1984-1985 lokacin mulkin soji ƙarƙashin marigayi Janar Muhammadu Buhari, ya kuma yi ƙoƙari gaya, wajen assasa taswirar gina sabuwar jihar Bauchi (roadmap).

 

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A saƙon ta’aziyya da ya fitar a ranar Lahadi ɗauke da sanya hannun babban hadiminsa a ɓangaren hulda da ‘yan jarida, Kwamared Mukhtar Gidado, gwamnan ya misalta marigayin a matsayin babban jigo, uba, dattijon kwarai, sarki mai daraja wanda ya bada gagarumin gudunmawa wajen hidimta wa ƙasar nan cikin gaskiya, riƙon amana da tsoron Allah.

 

Ya lura kan cewa tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a lokacin da take haɗe da Bauchi da Gombe ya taka rawa sosai wajen aza tunanin ci gaban jihar wanda har jihar ta kawo yanzu cikin nasara.

 

Ya ƙara da cewa lallai za a jima ba a mance irin gudunmawar da marigayin ya bayar a ɓangaren aikin soja da hidimar da ya yi a mulkinsa na farar hula.

 

“A zamaninsa ya yi mulki cikin gaskiya, janyo kowa a jika, tabbatar da adalci da daidaito a ɓangaren jagoranci,” gwamnan ya shaida.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa hatta a lokacin da ya ke Sarkin Zuru, Manjo janar Sami ya ci gaba da ɗabbaka halayensa ta kwarai, himmatuwa wajen hidima wa jama’a, son jama’a, jin ƙansu da tausayinsu a shugabancinsa a matsayin Sarki wanda ya yi cikin tsoron Allah.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa kura-kuransa kana ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi, rundunar sojan Nijeriya, da ma al’ummar ƙasa bisa wannan babban rashin.

 

“A madadin ɗaukacin al’ummar jihar Bauchi, gwamnati da masu riƙe da sarautun gargajiya, dama dukkanin gwamnonin jam’iyar PDP, ina miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi, Masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi da ma Daular Uthmaniyya kan wannan babban rashi, tare da addu’ar Allah yayi masa Rahama, da afuwa, da ba shi dacewa. Amin,” gwamnan ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jam’iyyar APC Ta Lashe Zaɓen Kujerun ‘Yan Majalisun Zariya Da Basawa

Next Post

Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

43 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

9 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

10 hours ago
Next Post
Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Daje Na Jam'iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.