ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Gwamnan Bauchi A Zamanin Mulkin Soja

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya nuna matuƙar ƙaduwa da samun labarin rasuwar Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), Sarkin Zuru da ke jihar Kebbi kuma tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a zamanin mulkin soja, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 82 a duniya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya. 

 

Gwamnan ya ce, “Dukkanin abinda muka samu daga Allah ne, haka ma wanda muka rasa, sai dai mu miƙa komai gare shi domin samun dacewa. Mun wayi gari da rasuwar shugaba, uba, jagora kuma abin koyi, tsohon gwamnan jiharmu ta Bauchi a mulkin soji, kuma mai martaba Sarkin Zuru, Manjo Janar Sani Sami (rtd).”

ADVERTISEMENT
  • Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
  • Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Gwamnan ya ƙara da cewa (Baba) Sami ya mulki jihar Bauchi daga 1984-1985 lokacin mulkin soji ƙarƙashin marigayi Janar Muhammadu Buhari, ya kuma yi ƙoƙari gaya, wajen assasa taswirar gina sabuwar jihar Bauchi (roadmap).

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

A saƙon ta’aziyya da ya fitar a ranar Lahadi ɗauke da sanya hannun babban hadiminsa a ɓangaren hulda da ‘yan jarida, Kwamared Mukhtar Gidado, gwamnan ya misalta marigayin a matsayin babban jigo, uba, dattijon kwarai, sarki mai daraja wanda ya bada gagarumin gudunmawa wajen hidimta wa ƙasar nan cikin gaskiya, riƙon amana da tsoron Allah.

 

Ya lura kan cewa tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a lokacin da take haɗe da Bauchi da Gombe ya taka rawa sosai wajen aza tunanin ci gaban jihar wanda har jihar ta kawo yanzu cikin nasara.

 

Ya ƙara da cewa lallai za a jima ba a mance irin gudunmawar da marigayin ya bayar a ɓangaren aikin soja da hidimar da ya yi a mulkinsa na farar hula.

 

“A zamaninsa ya yi mulki cikin gaskiya, janyo kowa a jika, tabbatar da adalci da daidaito a ɓangaren jagoranci,” gwamnan ya shaida.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa hatta a lokacin da ya ke Sarkin Zuru, Manjo janar Sami ya ci gaba da ɗabbaka halayensa ta kwarai, himmatuwa wajen hidima wa jama’a, son jama’a, jin ƙansu da tausayinsu a shugabancinsa a matsayin Sarki wanda ya yi cikin tsoron Allah.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa kura-kuransa kana ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi, rundunar sojan Nijeriya, da ma al’ummar ƙasa bisa wannan babban rashin.

 

“A madadin ɗaukacin al’ummar jihar Bauchi, gwamnati da masu riƙe da sarautun gargajiya, dama dukkanin gwamnonin jam’iyar PDP, ina miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi, Masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi da ma Daular Uthmaniyya kan wannan babban rashi, tare da addu’ar Allah yayi masa Rahama, da afuwa, da ba shi dacewa. Amin,” gwamnan ya shaida.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sulaiman
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Sulaiman
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Sulaiman
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

MASU ALAKA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Next Post
Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Daje Na Jam'iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.