ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Gwamnan Bauchi A Zamanin Mulkin Soja

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya nuna matuƙar ƙaduwa da samun labarin rasuwar Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), Sarkin Zuru da ke jihar Kebbi kuma tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a zamanin mulkin soja, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 82 a duniya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya. 

 

Gwamnan ya ce, “Dukkanin abinda muka samu daga Allah ne, haka ma wanda muka rasa, sai dai mu miƙa komai gare shi domin samun dacewa. Mun wayi gari da rasuwar shugaba, uba, jagora kuma abin koyi, tsohon gwamnan jiharmu ta Bauchi a mulkin soji, kuma mai martaba Sarkin Zuru, Manjo Janar Sani Sami (rtd).”

ADVERTISEMENT
  • Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
  • Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Gwamnan ya ƙara da cewa (Baba) Sami ya mulki jihar Bauchi daga 1984-1985 lokacin mulkin soji ƙarƙashin marigayi Janar Muhammadu Buhari, ya kuma yi ƙoƙari gaya, wajen assasa taswirar gina sabuwar jihar Bauchi (roadmap).

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

A saƙon ta’aziyya da ya fitar a ranar Lahadi ɗauke da sanya hannun babban hadiminsa a ɓangaren hulda da ‘yan jarida, Kwamared Mukhtar Gidado, gwamnan ya misalta marigayin a matsayin babban jigo, uba, dattijon kwarai, sarki mai daraja wanda ya bada gagarumin gudunmawa wajen hidimta wa ƙasar nan cikin gaskiya, riƙon amana da tsoron Allah.

 

Ya lura kan cewa tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a lokacin da take haɗe da Bauchi da Gombe ya taka rawa sosai wajen aza tunanin ci gaban jihar wanda har jihar ta kawo yanzu cikin nasara.

 

Ya ƙara da cewa lallai za a jima ba a mance irin gudunmawar da marigayin ya bayar a ɓangaren aikin soja da hidimar da ya yi a mulkinsa na farar hula.

 

“A zamaninsa ya yi mulki cikin gaskiya, janyo kowa a jika, tabbatar da adalci da daidaito a ɓangaren jagoranci,” gwamnan ya shaida.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa hatta a lokacin da ya ke Sarkin Zuru, Manjo janar Sami ya ci gaba da ɗabbaka halayensa ta kwarai, himmatuwa wajen hidima wa jama’a, son jama’a, jin ƙansu da tausayinsu a shugabancinsa a matsayin Sarki wanda ya yi cikin tsoron Allah.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa kura-kuransa kana ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi, rundunar sojan Nijeriya, da ma al’ummar ƙasa bisa wannan babban rashin.

 

“A madadin ɗaukacin al’ummar jihar Bauchi, gwamnati da masu riƙe da sarautun gargajiya, dama dukkanin gwamnonin jam’iyar PDP, ina miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi, Masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi da ma Daular Uthmaniyya kan wannan babban rashi, tare da addu’ar Allah yayi masa Rahama, da afuwa, da ba shi dacewa. Amin,” gwamnan ya shaida.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna
Labarai

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026
Labarai

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
Next Post
Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Daje Na Jam'iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.