ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Gwamnan Bauchi A Zamanin Mulkin Soja

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
11 months ago
Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya nuna matuƙar ƙaduwa da samun labarin rasuwar Manjo Janar Muhammadu Sani Sami (mai ritaya), Sarkin Zuru da ke jihar Kebbi kuma tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a zamanin mulkin soja, wanda ya rasu a ranar Lahadi yana da shekaru 82 a duniya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya. 

 

Gwamnan ya ce, “Dukkanin abinda muka samu daga Allah ne, haka ma wanda muka rasa, sai dai mu miƙa komai gare shi domin samun dacewa. Mun wayi gari da rasuwar shugaba, uba, jagora kuma abin koyi, tsohon gwamnan jiharmu ta Bauchi a mulkin soji, kuma mai martaba Sarkin Zuru, Manjo Janar Sani Sami (rtd).”

ADVERTISEMENT
  • Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
  • Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Gwamnan ya ƙara da cewa (Baba) Sami ya mulki jihar Bauchi daga 1984-1985 lokacin mulkin soji ƙarƙashin marigayi Janar Muhammadu Buhari, ya kuma yi ƙoƙari gaya, wajen assasa taswirar gina sabuwar jihar Bauchi (roadmap).

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

A saƙon ta’aziyya da ya fitar a ranar Lahadi ɗauke da sanya hannun babban hadiminsa a ɓangaren hulda da ‘yan jarida, Kwamared Mukhtar Gidado, gwamnan ya misalta marigayin a matsayin babban jigo, uba, dattijon kwarai, sarki mai daraja wanda ya bada gagarumin gudunmawa wajen hidimta wa ƙasar nan cikin gaskiya, riƙon amana da tsoron Allah.

 

Ya lura kan cewa tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bauchi a lokacin da take haɗe da Bauchi da Gombe ya taka rawa sosai wajen aza tunanin ci gaban jihar wanda har jihar ta kawo yanzu cikin nasara.

 

Ya ƙara da cewa lallai za a jima ba a mance irin gudunmawar da marigayin ya bayar a ɓangaren aikin soja da hidimar da ya yi a mulkinsa na farar hula.

 

“A zamaninsa ya yi mulki cikin gaskiya, janyo kowa a jika, tabbatar da adalci da daidaito a ɓangaren jagoranci,” gwamnan ya shaida.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa hatta a lokacin da ya ke Sarkin Zuru, Manjo janar Sami ya ci gaba da ɗabbaka halayensa ta kwarai, himmatuwa wajen hidima wa jama’a, son jama’a, jin ƙansu da tausayinsu a shugabancinsa a matsayin Sarki wanda ya yi cikin tsoron Allah.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa kura-kuransa kana ya sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi, rundunar sojan Nijeriya, da ma al’ummar ƙasa bisa wannan babban rashin.

 

“A madadin ɗaukacin al’ummar jihar Bauchi, gwamnati da masu riƙe da sarautun gargajiya, dama dukkanin gwamnonin jam’iyar PDP, ina miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi, Masarautar Zuru, gwamnatin jihar Kebbi da ma Daular Uthmaniyya kan wannan babban rashi, tare da addu’ar Allah yayi masa Rahama, da afuwa, da ba shi dacewa. Amin,” gwamnan ya shaida.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

MASU ALAKA

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Labarai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Next Post
Daje Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

Daje Na Jam'iyyar APC Ya Lashe Zaɓen Majalisar Dokokin Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.