• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Buni Ya Haramta Amfani Da Motocin Gwamnati Ba A Lokacin Aiki Ba

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Buni Ya Haramta Amfani Da Motocin Gwamnati Ba A Lokacin Aiki Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya haramta wa ma’aikatan gwamnatin jihar amfani da motoci da kayan gwamnati wajen amfanin kansu ba a lokacin aiki ba.

Gwamna Buni ya bayyana hakan bayan ya rantsar da sabbin manyan sakatarorin guda 9, ranar Talata inda kuma ya bukaci su yi amfani da ilimi da basirarsu wajen inganta aikin gwamnati a ma’aikatun da aka tura su don ci gaban jihar.

  • Gwamna Buni Na Jam’iyyar APC Ya Lashe Zaben Gwamnan Jihar Yobe

Buni ya kara da cewa za a yi amfani da motocin gwamnati ne wajen ayyukan gwamnati kawai tare da bai wa sakataren gwamnatin jiha, shugaban ma’aikata da umurnin su tabbatar an bi wannan ka’ida.

Ya ce, “Gwamnati ba za ta lamunci almubazzaranci da karkatar da dukiyar gwamnati wajen yin zagon kasa ga kokarinmu na samar da ayyuka ga jama’a ba.”

Ya kuma umurci dukkanin manyan sakatarorin da su kasance ‘yan kasa nagari, su yi aiki tare da kwamishinoninsu da daraktoci da sauran ma’aikata a ma’aikatu da sassansu domin cimma burin da aka sa gaba domin samun sakamako mai ma’ana.

Labarai Masu Nasaba

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

A cewarsa, ana sa ran a matsayinsu na jigo a tafiyar da ayyukan gwamnti, za su bai wa maras da kunya wajen nuna kwazo da bajinta da kwarewarsu domin cimma burin da aka sanya a gaba, da kuma gudanar da ayyukan da ake bukata cikin inganci ga al’ummar jihar.

“Kwanan nan gwamnatinmu ta dauki sama da mutum 2,600 da suka kammala digiri, babbar difloma da karamar difloma da NCE aiki domin cike gurbi a ma’aikatan gwamnati wajen bunkasa ayyukan yi.”

“Duk hanyoyin sadarwa da kai-komo na fayal-fayal dole ne su bi kai’idoji da tsare-tsaren da suka dace. Saboda bai kamata a rika sakin fayal-fayal din gwamnati ga mutanen da ka’idar aikin gwamnati bai ba su da izini ba. Na umurci sakataren gwamnatin jiha da ya lura kuma ya yi aiki yadda ya kamata kan haka.”

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Yobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

Next Post

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Cardoso A Matsayin Sabon Gwamnan CBN

Related

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

1 hour ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

4 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

5 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

6 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

7 hours ago
Next Post
Cardoso

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Cardoso A Matsayin Sabon Gwamnan CBN

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.