• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

Za a samar da sashen da zai kunshi gadaje 200

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da aikin sake gina babban asibitin Ƙaramar Hukumar Talata Mafara da samar da katafaren ginin da zai ɗauki gadaje 200.

A yayin ƙaddamarwar, gwamnan ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta kiwon lafiya a jihar, tare da bayyana irin rawar da manyan asibitoci ke takawa a fannin kiwon lafiya.

Mallam Yahaya Abdulkarim, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato ne babban baƙo na musamman a wajen bikin ƙaddamarwar.

Gwamna Dauda Lawal, ya bayyana damuwarsa kan yadda aka yi watsi da babban asibitin Talatan Mafara, inda ya nuna cewa asibitin na fama da rashin isassun kayan aikin jinya da kuma rashin kyawun ababen more rayuwa a tsawon shekaru.

Ya ce gwamnatocin baya sun yi watsi da harkar kiwon lafiya gaba ɗaya, wanda hakan ya sa gwamnatinsa ta fara aiwatar da aikin gyara fannin.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

“Da yardar Allah yau na zo ne domin cika alƙawarin da na ɗauka a watannin baya lokacin da na ziyarci wannan asibiti da jami’ar jihar. Bisa la’akari da halin da ake ciki a wannan cibiyar kiwon lafiya, na yi alƙawarin gudanar da aikin sake gina shi gaba ɗaya don samar da babban asibitin da ya dace da babban gari kamar Talata Mafara.

“Gwamnatinmu ta ba da fifiko wajen farfaɗo da ababen more rayuwa a matsayin muhimmin ginshiƙin ajandar kawo sauyi. Mun sanya ilimi da kiwon lafiya a kan gaba, tare da sanin matsayinsu wajen ci gaban al’umma. Wannan asibiti ɗaya ne daga cikin wurare da yawa da ake ginawa don samar da yanayi mai kyau wajen samar da nagartaccen ayyukan kiwon lafiya.

  • Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

 

“Gwamnatinmu ta tsaya tsayin daka wajen sanya hannun jari a fannin kiwon lafiya, tare da fahimtar muhimmiyar rawar da manyan asibitocin ke takawa a tsarin samar da lafiya. Suna aiki a matsayin muhimman hanyoyin da suka haɗa cibiyoyin Kula da Lafiya na Farko da Manyan Cibiyoyin Kiwon Lafiya.

“Aikin da muke ƙaddamarwa a yau ya ƙunshi gina asibiti mai ɗaukar gadaje 200 tare da samar da kayan aiki na zamani domin inganta lafiyar al’umma.

“Ya haɗa da gine-gine kamar haka: Wuraren zaman jira, sashin bayanai da asusun ajiya, sashen kula da yara, ɗakin jinya na maza, ɗakin jinya na mazan da aka yi wa tiyata, ɗakin gwaje-gwaje, ɗakin tiyata, ɗakin gwaje-gwajen haƙori, ɗakin karɓar magani, ɗakin jinya na matan da aka yi wa tiyata, ɗakin jinya na mata, sashen ENT. Ɗakunan haihuwa guda biyu tare da ofishin babbar mai karɓar haihuwa, ɗakin wankin ciwo, ɗakin zaman ma’aikatan jinya, ofishin Babban Manajan Daraktan Kiwon Lafiya na asibitin tare da ofishin sakatarensa, ofishin likitan haƙori, ɗakin canja kaya na mata, ɗakunan ganin likita guda biyar, ɗakin ICU, rukunin na’urar X-ray, sashen kai marasa lafiya na gaggawa ‘Accident & Emergency (A&E)’, sashen kula da masu juna biyu, wurin cin abinci, da ofishin matron.

“Za a kammala shi cikin watanni shida, inda kamfanin Abdulwahab Razaq Memorial Ltd ya kasance a matsayin ɗan kwangilar. A halin da ake ciki, abin farin ciki ne na musamman na gayyato babban baƙon mu, mai girma tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Malam Yahaya Abdulkarim, Magajin Rafin Sokoto, domin ƙaddamar da aikin gina wannan asibiti a hukumance.”

Tun da farko, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Malam Yahaya Abdulkarim, ya yaba wa gwamna Dauda Lawal bisa bai wa ɓangaren kiwon lafiya fifiko a cikin ayyukan da gwamnatinsa ta sa gaba. “Na yi mamakin lokacin da gwamnan ya shaida min cewa an riga an sayo dukkan kayan aikin da za a yi amfani da su a Babban Asibitin, wannan abin yabawa ne matuƙa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsibitiGwamna Dauda LawalgwamnatiGwamnatociKiwon LafiyaTalata MafaraZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adawar Siyasa A Jihar Sakkwato Da Sauran Lamurra

Next Post

Rushewar Gine-gine Ta Yi Sanadiyar Rasuwar Mutane Fiye Da 90 A Shekara Daya

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

6 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

8 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

10 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

13 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

16 hours ago
Next Post
Rushewar Gine-gine Ta Yi Sanadiyar Rasuwar Mutane Fiye Da 90 A Shekara Daya

Rushewar Gine-gine Ta Yi Sanadiyar Rasuwar Mutane Fiye Da 90 A Shekara Daya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.