ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ziyarci Yankunan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Gummi

by Leadership Hausa
2 years ago
ambaliya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya kai ziyarar gani da ido zuwa yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Gummi ta Jihar.

A makon da ya gabata ne mamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a wasu yankunan ƙaramar hukumar Gummi, inda ya lalata gidaje da dama.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce tawagar gwamna Lawal ta fara ne da gaisuwar ban girma ga fadar Mai Martaba Sarkin Gummi, Mai Shari’a Lawal Hassan.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, gwamnan ya zagaya garin Gummi ne domin jajanta wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa kafin ya wuce garin Gayari domin duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

ambaliya

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Gwamna Lawal ya nuna matuƙar damuwa bayan duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Ya ƙara da cewe, tuni tawagar injiniyoyi suka fara bincike a yankunan domin samun mafita mai ɗorewa.

“A yau, na zo ƙaramar hukumar Gummi ne domin yin jaje tare da gudanar da ziyarar gani da ido a yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a makon jiya.

“Nan da nan bayan na samu labarin faruwar lamarin, sai na aika kwamishinoni biyu domin su kai ziyara kuma su jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa.

ambaliya

“Bayan ziyarar mataimakin gwamna, na tura tawagar injiniyoyi domin su duba tare da sanin musabbabin ambaliyar ruwa.

“Yana da muhimmanci a lura cewa na ba da umarnin a fara aiki nan take don daƙile faruwar irin wannna matsalar a nan gaba.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen sanar da ku cewa na bayar da gudunmawar buhunan abinci guda 10,000 da suka haɗa da shinkafa, masara, da gero, domin raba wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa. Yanzu haka manyan motocin na kan hanyar Gummi domin a raba wa al’umma.

ambaliya

“Ni kuma a madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina tallafa wa waɗanda abin ya shafa da Naira Miliyan 100. Bugu da ƙari, duk waɗanda abin ya shafa, za a raba musu filaye nesa da yankin da ke da haɗari domin su gina sabbin gidaje.”

ambaliya
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar Kuɗin Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki - Masana

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.